• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Uwar Da Ta Kashe ‘Ya’yanta Daurin Rai Da Rai A Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Amurka

An yanke wa wata uwa mazauniyar Jihar Idaho ta Amurka da ke cikin wata kungiyar asiri ta masu hasashen aukuwar bala’i, hukuncin daurin rai da rai a gidan yari bayan an same ta da laifin kashe ‘ya’yanta masu tasowa biyu tare da hada baki wajen kashe kishiyarta.

An samu Lori Ballow Daybell, mai shekara 50, da aikata babban laifin kisan kai da tuhume-tuhume hada baki don aikata laifi a watan Mayu.

  • Hanyoyin Da Suka Kamata ECOWAS Ta Bi Wajen Warware Rikicin Nijar
  • Warware Jita-jita Masu Alaka Da Kwararon Roba (Condom)

Lori Ballow ta kashe danta Joshua wanda ake yi wa lakabi da “JJ” Ballow, dan shekara bakwai da ‘yarta Tylee Ryan ‘yar shekara 16.

An gano gawawwakinsu ne binne a cikin gidan mijinta Chad Daybell a shekara ta 2020.

A ranar Litinin, Mai shari’a Steben Boyce ya yanke wa Lori Ballow hukuncin daurin rai da rai har sau uku, ba tare da yiwuwar samun sakin je-ka-mu-ga-hankalinka ba.

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

“Kisan kai mafi munin da ba za a iya kwatantawa ba shi ne wanda uwa za ta halaka ‘ya’yan cikinta, kuma shi ne hakikanin abin da kika aikata,” Mai shari’a Boyce ya ce,

Kotu ta saurari bayanan shaidu masu ratsa zuciya daga dangin mijinta a lokacin yanke hukuncin.

“Tylee da JJ sun kawo dumbin haske a wannan duniya,” Colby Ryan, wani babban ‘ya’yansu ya fada a cikin wani jawabi da masu shigar da kara suka karanta.

“Ina son a rika tunawa da su kamar yadda Allah ya halicce su amma ba a matsayin wani abin kallo ko abin buga labarinsu a jaridun duniya ba.”

Mijinta, Chad Daybell shi man an tuhume kan mutuwar ‘ya’yan da kuma mutuwar tsohuwar matarsa, Tammy Daybell, makonni kafin ya auri Lori Ballow. An tsara gudanar da shari’arsa a cikin shekara mai zuwa.

Chad Daybell marubuci ne da ya wallafa litattafan tashin duniya bisa koyarwar addinin Mormon.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga
Kasashen Ketare

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Next Post
Gwamnatin Zamfara Ta Kaddamar Da Gangamin Kula Da Lafiya Kyauta

Gwamnatin Zamfara Ta Kaddamar Da Gangamin Kula Da Lafiya Kyauta

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.