ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Binciken ‘Yansandan Da Suka Karbi Naira 40,000 Daga Hannun Wasu Fasinja

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Fasinja

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

ADVERTISEMENT

Wani mai amfani da shafin Twitter @LifeOfNapaul ya zargi wasu ‘yansanda da karbar Naira 40,000 daga wurinsa da wasu mutum uku a Jihar Ribas.

Da yake bayyana irin halin da ya tsinci kansa a wani sako inda ya buya ya wallafa a shafinsa na Twitter a yammacin ranar Lahadi, mutumin ya ce ya hau motar haya ce akan hanyarsa ta zuwa Fatakwal, suna cikin tafiya ‘yansandan suka tsayar da motar suka fara bincikensa da wasu fasinjoji uku bisa zarginsu da aikata laifi.

  • Sin: Duk Wanda Ke Neman Fakewa Da Batun Hong Kong Don Hana Bunkasuwar Kasar Sin Ba Zai Yi Nasara ba
  • Gwamnonin Arewa Maso Yamma Sun Gana Da Tinubu Kan Matsalar Tsaro

Da yake lura da cewa ’yansandan ba su ga wani abu da ya shafi laifuka ba, sai  ‘yansandan suka bukaci Naira 50,000 wato shi ya ba da Naira 20,000 sauran abokan tafiyarsa kuma su ba da Naira 10,000 kowannensu kafin a bar su su ci gaba da tafiya.

Rubutun nasa ya ce, “Na gaji da irin wannan hali na ‘yansand, saboda irin wannan ta taba faruwa da ni aka kai ni ofishin ’yan sanda, aka hada ni da masu laifi kamar mai laifi, saboda kawai na ga ina amfani da wayar iPhone.

 “ Gashi yau (Lahadi) a kan hanyata ta zuwa Fatakwal a cikin motar haya an sake tar ni, aka ce mu dakata aka fito da mu aka bincike ni, aka bude hirar da na yi na WhatsApp daya bayan daya, da kowacce manhaja dake kan wayata aka bincke ba su samu komai na laifi ba.

 “Duk da hakan dai suka ce ba za su bar mu mu tafi sai ba da wani abu, mu hudu ne maza kawai a cikin matar kirar Sienna, sauran mata ne. Sai suka ce direban ya bar mu a wurin amma na yi ta rokon direban ya tsaya.”

Wanda abin ya shafa ya ce an shafe sama da sa’a guda ana ganar da muhawara, inda ya ce a lokacin da ya yi yunkurin neman hadin kan ‘yansandan domin sasanta lamarin cikin lumana, kawai sai suka buga masa ankwa a hannu.

Ya rubuta, “Dan uwa, ni fa ba mai laifi ba ne, sun ce suna tuhuma ta ne, na yi ta tambayar ‘ta yaya?’ A lokacin na fusata sosai.

Jami’an sun nemi a ba su Naira 50,000, daga karshe dai kowannenmu ya biya Naira Naira dubu 10, suka raba kudin kowannen su ya dauki Naira dubu 10. Abin da ya bani dariya shi ne wadannan da ake kira da jami’an tsaro sai ga su sun buge da kirga kudin da suka a wurin fasinja a gaban mutane.

“Asusun da na aika da kudin, lambar mace ce kuma na bincika Facebook na gano tana zaune a Abuja. Ban sami sunayensu ba, Hilud din da suka yi amfani da shi ba ta jami’in ‘yansandan Nijeriya ba ce kuma gaba daya ma motar ba ta da lamba.”

Wanda aka karbi kudin nasu ya makala hoton daya daga cikin ‘yansandan da ake zargi da karbar kudin a rubutun nasa.

Da yake mayar da martani, kwamandan rundunar ‘yansandan Jihar Ribas, a wani sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter, @RibersPoliceNG, ta ce kwamishinan ‘yansandan jihar, Nwonyi Emeka, ya yi Allah wadai da wannan hali da ‘yansandan suka nuna.

 “Kwamishanan ‘yansandan da muke da shi a Jihar Ribas ba shi da wata masaniya a kan irin wannan abin kunya da wadannan jami’ai ke yi, sannan ya sha alwashin gano jami’in tare da gurfanar da su gaban kuliya domin fuskantar hukuncin ladabtarwa, kuma ya yi alkawarin mayar muku da kudadenku,” in ji rundunar ‘yansandan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Next Post
Hade-haden Lemo Mai Dandano

Hade-haden Lemo Mai Dandano

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.