• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Binciken ‘Yansandan Da Suka Karbi Naira 40,000 Daga Hannun Wasu Fasinja

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wani mai amfani da shafin Twitter @LifeOfNapaul ya zargi wasu ‘yansanda da karbar Naira 40,000 daga wurinsa da wasu mutum uku a Jihar Ribas.

Da yake bayyana irin halin da ya tsinci kansa a wani sako inda ya buya ya wallafa a shafinsa na Twitter a yammacin ranar Lahadi, mutumin ya ce ya hau motar haya ce akan hanyarsa ta zuwa Fatakwal, suna cikin tafiya ‘yansandan suka tsayar da motar suka fara bincikensa da wasu fasinjoji uku bisa zarginsu da aikata laifi.

  • Sin: Duk Wanda Ke Neman Fakewa Da Batun Hong Kong Don Hana Bunkasuwar Kasar Sin Ba Zai Yi Nasara ba
  • Gwamnonin Arewa Maso Yamma Sun Gana Da Tinubu Kan Matsalar Tsaro

Da yake lura da cewa ’yansandan ba su ga wani abu da ya shafi laifuka ba, sai  ‘yansandan suka bukaci Naira 50,000 wato shi ya ba da Naira 20,000 sauran abokan tafiyarsa kuma su ba da Naira 10,000 kowannensu kafin a bar su su ci gaba da tafiya.

Rubutun nasa ya ce, “Na gaji da irin wannan hali na ‘yansand, saboda irin wannan ta taba faruwa da ni aka kai ni ofishin ’yan sanda, aka hada ni da masu laifi kamar mai laifi, saboda kawai na ga ina amfani da wayar iPhone.

 “ Gashi yau (Lahadi) a kan hanyata ta zuwa Fatakwal a cikin motar haya an sake tar ni, aka ce mu dakata aka fito da mu aka bincike ni, aka bude hirar da na yi na WhatsApp daya bayan daya, da kowacce manhaja dake kan wayata aka bincke ba su samu komai na laifi ba.

 “Duk da hakan dai suka ce ba za su bar mu mu tafi sai ba da wani abu, mu hudu ne maza kawai a cikin matar kirar Sienna, sauran mata ne. Sai suka ce direban ya bar mu a wurin amma na yi ta rokon direban ya tsaya.”

Wanda abin ya shafa ya ce an shafe sama da sa’a guda ana ganar da muhawara, inda ya ce a lokacin da ya yi yunkurin neman hadin kan ‘yansandan domin sasanta lamarin cikin lumana, kawai sai suka buga masa ankwa a hannu.

Ya rubuta, “Dan uwa, ni fa ba mai laifi ba ne, sun ce suna tuhuma ta ne, na yi ta tambayar ‘ta yaya?’ A lokacin na fusata sosai.

Jami’an sun nemi a ba su Naira 50,000, daga karshe dai kowannenmu ya biya Naira Naira dubu 10, suka raba kudin kowannen su ya dauki Naira dubu 10. Abin da ya bani dariya shi ne wadannan da ake kira da jami’an tsaro sai ga su sun buge da kirga kudin da suka a wurin fasinja a gaban mutane.

“Asusun da na aika da kudin, lambar mace ce kuma na bincika Facebook na gano tana zaune a Abuja. Ban sami sunayensu ba, Hilud din da suka yi amfani da shi ba ta jami’in ‘yansandan Nijeriya ba ce kuma gaba daya ma motar ba ta da lamba.”

Wanda aka karbi kudin nasu ya makala hoton daya daga cikin ‘yansandan da ake zargi da karbar kudin a rubutun nasa.

Da yake mayar da martani, kwamandan rundunar ‘yansandan Jihar Ribas, a wani sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter, @RibersPoliceNG, ta ce kwamishinan ‘yansandan jihar, Nwonyi Emeka, ya yi Allah wadai da wannan hali da ‘yansandan suka nuna.

 “Kwamishanan ‘yansandan da muke da shi a Jihar Ribas ba shi da wata masaniya a kan irin wannan abin kunya da wadannan jami’ai ke yi, sannan ya sha alwashin gano jami’in tare da gurfanar da su gaban kuliya domin fuskantar hukuncin ladabtarwa, kuma ya yi alkawarin mayar muku da kudadenku,” in ji rundunar ‘yansandan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaBincikeFasinja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayern Munich Na Duba Yiwuwar Daukar Kyle Walker

Next Post

Hade-haden Lemo Mai Dandano

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

4 days ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 month ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 month ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
Next Post
Hade-haden Lemo Mai Dandano

Hade-haden Lemo Mai Dandano

LABARAI MASU NASABA

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

July 9, 2025
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.