ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Binciken ‘Yansandan Da Suka Karbi Naira 40,000 Daga Hannun Wasu Fasinja

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Fasinja

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Wani mai amfani da shafin Twitter @LifeOfNapaul ya zargi wasu ‘yansanda da karbar Naira 40,000 daga wurinsa da wasu mutum uku a Jihar Ribas.

Da yake bayyana irin halin da ya tsinci kansa a wani sako inda ya buya ya wallafa a shafinsa na Twitter a yammacin ranar Lahadi, mutumin ya ce ya hau motar haya ce akan hanyarsa ta zuwa Fatakwal, suna cikin tafiya ‘yansandan suka tsayar da motar suka fara bincikensa da wasu fasinjoji uku bisa zarginsu da aikata laifi.

  • Sin: Duk Wanda Ke Neman Fakewa Da Batun Hong Kong Don Hana Bunkasuwar Kasar Sin Ba Zai Yi Nasara ba
  • Gwamnonin Arewa Maso Yamma Sun Gana Da Tinubu Kan Matsalar Tsaro

Da yake lura da cewa ’yansandan ba su ga wani abu da ya shafi laifuka ba, sai  ‘yansandan suka bukaci Naira 50,000 wato shi ya ba da Naira 20,000 sauran abokan tafiyarsa kuma su ba da Naira 10,000 kowannensu kafin a bar su su ci gaba da tafiya.

Rubutun nasa ya ce, “Na gaji da irin wannan hali na ‘yansand, saboda irin wannan ta taba faruwa da ni aka kai ni ofishin ’yan sanda, aka hada ni da masu laifi kamar mai laifi, saboda kawai na ga ina amfani da wayar iPhone.

 “ Gashi yau (Lahadi) a kan hanyata ta zuwa Fatakwal a cikin motar haya an sake tar ni, aka ce mu dakata aka fito da mu aka bincike ni, aka bude hirar da na yi na WhatsApp daya bayan daya, da kowacce manhaja dake kan wayata aka bincke ba su samu komai na laifi ba.

 “Duk da hakan dai suka ce ba za su bar mu mu tafi sai ba da wani abu, mu hudu ne maza kawai a cikin matar kirar Sienna, sauran mata ne. Sai suka ce direban ya bar mu a wurin amma na yi ta rokon direban ya tsaya.”

Wanda abin ya shafa ya ce an shafe sama da sa’a guda ana ganar da muhawara, inda ya ce a lokacin da ya yi yunkurin neman hadin kan ‘yansandan domin sasanta lamarin cikin lumana, kawai sai suka buga masa ankwa a hannu.

Ya rubuta, “Dan uwa, ni fa ba mai laifi ba ne, sun ce suna tuhuma ta ne, na yi ta tambayar ‘ta yaya?’ A lokacin na fusata sosai.

Jami’an sun nemi a ba su Naira 50,000, daga karshe dai kowannenmu ya biya Naira Naira dubu 10, suka raba kudin kowannen su ya dauki Naira dubu 10. Abin da ya bani dariya shi ne wadannan da ake kira da jami’an tsaro sai ga su sun buge da kirga kudin da suka a wurin fasinja a gaban mutane.

“Asusun da na aika da kudin, lambar mace ce kuma na bincika Facebook na gano tana zaune a Abuja. Ban sami sunayensu ba, Hilud din da suka yi amfani da shi ba ta jami’in ‘yansandan Nijeriya ba ce kuma gaba daya ma motar ba ta da lamba.”

Wanda aka karbi kudin nasu ya makala hoton daya daga cikin ‘yansandan da ake zargi da karbar kudin a rubutun nasa.

Da yake mayar da martani, kwamandan rundunar ‘yansandan Jihar Ribas, a wani sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter, @RibersPoliceNG, ta ce kwamishinan ‘yansandan jihar, Nwonyi Emeka, ya yi Allah wadai da wannan hali da ‘yansandan suka nuna.

 “Kwamishanan ‘yansandan da muke da shi a Jihar Ribas ba shi da wata masaniya a kan irin wannan abin kunya da wadannan jami’ai ke yi, sannan ya sha alwashin gano jami’in tare da gurfanar da su gaban kuliya domin fuskantar hukuncin ladabtarwa, kuma ya yi alkawarin mayar muku da kudadenku,” in ji rundunar ‘yansandan.

Fasinja
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Hade-haden Lemo Mai Dandano

Hade-haden Lemo Mai Dandano

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.