ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Binciken ‘Yansandan Da Suka Karbi Naira 40,000 Daga Hannun Wasu Fasinja

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Fasinja

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Wani mai amfani da shafin Twitter @LifeOfNapaul ya zargi wasu ‘yansanda da karbar Naira 40,000 daga wurinsa da wasu mutum uku a Jihar Ribas.

Da yake bayyana irin halin da ya tsinci kansa a wani sako inda ya buya ya wallafa a shafinsa na Twitter a yammacin ranar Lahadi, mutumin ya ce ya hau motar haya ce akan hanyarsa ta zuwa Fatakwal, suna cikin tafiya ‘yansandan suka tsayar da motar suka fara bincikensa da wasu fasinjoji uku bisa zarginsu da aikata laifi.

  • Sin: Duk Wanda Ke Neman Fakewa Da Batun Hong Kong Don Hana Bunkasuwar Kasar Sin Ba Zai Yi Nasara ba
  • Gwamnonin Arewa Maso Yamma Sun Gana Da Tinubu Kan Matsalar Tsaro

Da yake lura da cewa ’yansandan ba su ga wani abu da ya shafi laifuka ba, sai  ‘yansandan suka bukaci Naira 50,000 wato shi ya ba da Naira 20,000 sauran abokan tafiyarsa kuma su ba da Naira 10,000 kowannensu kafin a bar su su ci gaba da tafiya.

Rubutun nasa ya ce, “Na gaji da irin wannan hali na ‘yansand, saboda irin wannan ta taba faruwa da ni aka kai ni ofishin ’yan sanda, aka hada ni da masu laifi kamar mai laifi, saboda kawai na ga ina amfani da wayar iPhone.

 “ Gashi yau (Lahadi) a kan hanyata ta zuwa Fatakwal a cikin motar haya an sake tar ni, aka ce mu dakata aka fito da mu aka bincike ni, aka bude hirar da na yi na WhatsApp daya bayan daya, da kowacce manhaja dake kan wayata aka bincke ba su samu komai na laifi ba.

 “Duk da hakan dai suka ce ba za su bar mu mu tafi sai ba da wani abu, mu hudu ne maza kawai a cikin matar kirar Sienna, sauran mata ne. Sai suka ce direban ya bar mu a wurin amma na yi ta rokon direban ya tsaya.”

Wanda abin ya shafa ya ce an shafe sama da sa’a guda ana ganar da muhawara, inda ya ce a lokacin da ya yi yunkurin neman hadin kan ‘yansandan domin sasanta lamarin cikin lumana, kawai sai suka buga masa ankwa a hannu.

Ya rubuta, “Dan uwa, ni fa ba mai laifi ba ne, sun ce suna tuhuma ta ne, na yi ta tambayar ‘ta yaya?’ A lokacin na fusata sosai.

Jami’an sun nemi a ba su Naira 50,000, daga karshe dai kowannenmu ya biya Naira Naira dubu 10, suka raba kudin kowannen su ya dauki Naira dubu 10. Abin da ya bani dariya shi ne wadannan da ake kira da jami’an tsaro sai ga su sun buge da kirga kudin da suka a wurin fasinja a gaban mutane.

“Asusun da na aika da kudin, lambar mace ce kuma na bincika Facebook na gano tana zaune a Abuja. Ban sami sunayensu ba, Hilud din da suka yi amfani da shi ba ta jami’in ‘yansandan Nijeriya ba ce kuma gaba daya ma motar ba ta da lamba.”

Wanda aka karbi kudin nasu ya makala hoton daya daga cikin ‘yansandan da ake zargi da karbar kudin a rubutun nasa.

Da yake mayar da martani, kwamandan rundunar ‘yansandan Jihar Ribas, a wani sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter, @RibersPoliceNG, ta ce kwamishinan ‘yansandan jihar, Nwonyi Emeka, ya yi Allah wadai da wannan hali da ‘yansandan suka nuna.

 “Kwamishanan ‘yansandan da muke da shi a Jihar Ribas ba shi da wata masaniya a kan irin wannan abin kunya da wadannan jami’ai ke yi, sannan ya sha alwashin gano jami’in tare da gurfanar da su gaban kuliya domin fuskantar hukuncin ladabtarwa, kuma ya yi alkawarin mayar muku da kudadenku,” in ji rundunar ‘yansandan.

Fasinja
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Hade-haden Lemo Mai Dandano

Hade-haden Lemo Mai Dandano

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.