• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Da PDP, Duk Kanwar Ja Ce -Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kiraye-kirayen Maye Ganduje Da Kwankwaso: Dattawan APC Sun Mayar Da Martani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana cewa APC da PDP dan juma ne da dan jummai sun gaza, a yanzu jam’iyyarsa ce kadai mafita ga ‘yan Nijeriya.

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya bayyana hakan ne a wurin babban taron jam’iyyar NNPP na kasa da ya gudana a Abuja.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Ya Kamata Jama’a Su Hada Kai Don Ciyar Da Nijeriya Gaba – Tinubu

Babban taron jam’iyyar ya samu halartar mambobin kwamitin zartarwa na jam’iyyar da shugabanninta na jihohi 36 ciki har da na Abuja da ‘yan majalisun jihohi, wanda aka tabbatar da zaben Ajuji Ahmed a matsayin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa tare da tabbatar da kundin tsarin jam’iyyar da kuma sauya alaman tambarin jam’iyyar.

Kwankwaso ya siffanta APC da PDP a matsayin taron tsintsiya babu shara, wanda suka tara jiga-jigan ‘yan siyasa marasa amfani tare da kawo kuncin rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Ya ce PDP jam’iyya ce da ta gaza, yayin da a yanzu gazawar APC ya fito kuru-kuru.

Ya tabbatar da cewa NNPP ce jam’iyya daya tilo da take kara bukasa a Nijeriya wacce ta fahimci muhimmancin ilimi wajen kawar da fatara da kuncin rayuwa da kuma yadda za a tsare rayukan da dukiyoyin ‘yan Nijeriya, ta hanyar tabbatar da hadin kai da kawo zaman lafiya da kuma wadata ga daukacin ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

“Dukkanmu mun san cewa PDP ta gaza. Mafi yawancinmu mun yanke shawara a tsakanin 2014 da 2015 mu kawo sauyi mai ma’ana. Abun takaicin dai shi ne, mun ga abubuwan da suka faru a tsakanin 2015 har zuwa yau. Wannan babban abun kunya ne ga gwamnatin APC. Saboda haka, mu a wurinmu, mun tabbatar da cewa APC ta gaza. Mun yi imani da cewa wannan kasar tana bukatar samun sauyi daga APC da PDP, kuma jam’iyyar NNPP ce kadai mafita, domin ita ce a yanzu take bunkasa a duk fadin kasar nan.

“Haka kuma na tabbatar da cewa wannan shi ne kyakkyawan fata kamar yadda muka tsaya a yau. Mafi yawancin bangarorin kasar nan, musamman yankin Arewacin Nijeriya, yanki da na fito, mafi yawan mutane an kore su daga gidajensu, sannan an kashe mutane da dama. A yanzu haka wasu suna raywa ne a cikin dazuka sakamakon garkuwa da su da ‘yan bindiga suka yi da kuma sauran ayyukan ta’addanci. Sannan mafi yawancin mutane ba sa damuwa da hakan. Abun sauki ne a yi garkuwa da mutane a gidagensu ko kan hanya ko kuma a kasuwa. Na tabbatar da cewa a kasar nan ne kadai ake irin wannan mummunan dabi’a. Hakkin gwamnati ne ta kare rayuwakan ‘yan kasa da kuma dukiyoyinsu.

“A matsayina na tsohon ministan tsaro kuma babban hafsan tsaro na Jihar Kano tsawon shekara 8 na tabbatar kuna da kayan aiki da jami’an tsaro da za su iya kawo tsaro a kasar nan. Wannan dama ce a gare ni wajen ganin mun hada kai mun yi karfi na ceto Nijeriya. Ina mai tabbatar da cewa za a ci gaba da samun hadin kai a cikin wannan jam’iyyar tamu. Za a ci gaba da yi wa dukkan ‘ya’yan jam’iyyar adalci. Za mu ci gaba da gudanar da zaben fitar da gwani a wannan jam’iyya domin bai wa kowa damar samun matsayi.

“Ina godiya ga dukkaninku da kuka zabe ni a matsayin jagoran jam’iyyar na kasa a jam’iyyarmu. Ina alfahari da hakan. Sannan ina mai tabbatar muku cewa zai yi duk mai yuwuwa wajen tabbatar da cewa wannan jam’iyya ta kara karfi sosai,” in ji Kwankwaso.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Gana Da Shugaban Kasar Suriname

Next Post

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

'Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

LABARAI MASU NASABA

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

August 7, 2025
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

August 7, 2025
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.