• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa A Jihar Kebbi

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Atiku Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa A Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya yi nasarar lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar ranar Asabar a Kebbi da kuri’u 285,175.

Jami’in tattara sakamakon zaben na jihar, Farfesa Usman Sa’idu a lokacin da yake gabatar da sakamakon a Birnin Kebbi, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Sanata Bola Tinubu ya samu kuri’u 248,088.

  • Tawagar Masu Aikin Jinya Ta Kasar Sin Dake Kasar Togo Ta Yi Aikin Jinya Kyauta
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Rawa Wajen Daidaita Matsalar Basussukan Zambiya

Saidu ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, shi ma ya samu kuri’u 10,682 yayin da jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), ya samu kuri’u 5,038.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan bayyana sakamakon, babban daraktan yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a Jihar Kebbi, Alhaji Bala Dole ya bayyana jin dadinsa da hakan.

Ya yi iƙirarin cewa idan ba don wasu “kananan kura-kurai” da jam’iyyarsa ta samu kuri’u masu yawan gaske.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Hakazalika, Wakilin jam’iyyar APC, Alhaji Ja’afar Ahmed, ya ce akwai batutuwan da suka shafi sakamakon, inda ya jaddada cewa, wannan zaben na da nasaba da tashin hankali, rashin zuwan kayan zabe, rashin aiki na BIVAS da kuma jawo hankalin jama’a ta fuskoki daban-daban.

Da yake mayar da martani, Kwamishinan Zabe na Jihar, Alhaji Ahmed Bello-Mahmud, ya bayyana jin dadinsa da cewa an gudanar da zabukan cikin kwanciyar hankali, adalci, gaskiya da kuma kammalawa ba tare da wata tangarda ba.

Ya kuma yi kira ga masu zabe da su ci gaba da gudanar da zabuka masu zuwa domin amfanin kowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuKebbiSaben Shugaban KasaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tawagar Masu Aikin Jinya Ta Kasar Sin Dake Kasar Togo Ta Yi Aikin Jinya Kyauta

Next Post

Kwankwaso Ya Lashe Kano, Ya Bai Wa Tinubu Da Atiku Gagarumar Tazara

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

16 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

24 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 day ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

2 days ago
Next Post
Kwankwaso Ya Lashe Kano, Ya Bai Wa Tinubu Da Atiku Gagarumar Tazara

Kwankwaso Ya Lashe Kano, Ya Bai Wa Tinubu Da Atiku Gagarumar Tazara

LABARAI MASU NASABA

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.