• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Hanyoyin Gwamnatin Tarayya Da Aka Yi Watsi Da Su A Jihohin Arewa 14

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Labarai
0
Ayyukan Hanyoyin Gwamnatin Tarayya Da Aka Yi Watsi Da Su A Jihohin Arewa 14
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu ababen hawa da mazauna jihohin Arewa 14 da aka yi watsi da ayyukan hanyoyin gwamnatin tarayya a jihohinsu sun yi kira ga Shugaban kasa Bola Tinubu da ministan ayyuka, Injiniya Dabid Umahi, kan halin da suke ciki na kunci bisa tabarbarewar hanyoyin gwamnatin tarayya.

Wani bincike da LEADERSHIP ta gudanar a jihohin Arewa 19 ya nuna cewa an bayar da kwangilar ayyukan manyan tituna da aka yi watsi da su tun bayan gwamnatin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo.

  • Munafurci Dodo Ne Me Shi Ya Kan Ci
  • Gwamnan Zamfara Ya Biya ‘Yan Fansho Hakkokinsu Fiye Da Nb7

Wasu kuma an yi watsi da ayyukan manyan titunan ne tun shekaru 10 da suka gabata na gwamnatocin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan da wanda ya gaje shi, Muhammadu Buhari.

Sai dai Jihar Borno, wadda har zuwa lokacin hada wannan rahoto a daren jiya ba a samu kammala rahotonta ba, sauran jihohin da abin ya shafa an yi watsi da ayyukan tituna ne a tsakanin biyu zuwa 10.

Jihohi hudu da suka hada da Kaduna, Kebbi, Taraba, da Zamfara su ne mafi karancin hanyoyin da aka yi watsi da su, yayin da Jihar Kwara ke da mafi yawan ayyukan hanyoyin da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa a karkashin jagorancin Tinubu.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

A Jihar Katsina kuwa, akwai kananan titunan gwamnatin tarayya da ke cikin mawuyacin hali, inda mafi yawansu ke bukatar gyara cikin gaggawa.

Titin Katsina zuwa Kano, wadda gwamnatin da ta shude ta bayar ba a kammala ba, ta tsaya a Gidan Mutun Daya.

Titin Mararaba Kankara zuwa Kankara a halin yanzu ana kan gyarawa, amma sauran muhimman hanyoyin ko dai an kasa gyarawa ko kuma ‘yan ta’adda sun mamayesu, wanda hakan ke kawo hadarurruka.

Titin Funtua zuwa Sheme dai ya shafe tsawon lokaci yana a lalace, lamarin da ya ta’azzara matsalar sace-sacen mutane da ake yi a yankin.

Haka zalika, titin Dutsinma zuwa Kankara, duk da cewa ana kulawa da shi sosai, ya zama yankin da ke fuskantar hadari saboda ‘yan fashin suna yi wa masu ababen hawa kwanton bauna tare da kai su dajin Rugu.

A Jihar Zamfara, babbar hanyar Jibiya zuwa Kaura Namoda, wacce a ake ganin hanya ce mai kyau da ta hada jihohin Katsina da Zamfara, amma a yanzu ta zama tarkon mutuwa saboda yawaitar ‘yan fashin daji.

A shekarar 2020, gwamnatin jihar ta ayyana shi a matsayin yankin da ba za a iya bi ba, tare da hana masu ababen hawa yin amfani da hanyar saboda yawaitar hare-haren ‘yan bindiga.

A Jihar Neja, kusan dukkan titunan gwamnatin tarayya sun lalace, wasu kuma gwamnatin jihar ta karbe su.

An shafe sama da shekaru 10 ana aikin titin Suleja zuwa Minna, wanda dan kwangilar ya yi watsi da shi tsawon shekaru uku, kafin ya koma aiki kimanin shekaru biyu da suka wuce. Ko da yake, binciken LEADERSHIP ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki nauyin gina sauran sassan hanyar da ta tashi daga Kakaki a karamar hukumar Paikoro zuwa Minna, babban birnin jihar, saboda tafiyar hawainiya da aikin hanyar yake yi.

Haka kuma bangaren Agaie-Bida na hanyar Lambata-Bida har yanzu yana cikin mummunan yanayi duk da cewa an bayar da kwangilolin hanyar kimanin shekaru biyar da suka gabata, haka ma hanyoyin Mokwa-Jebba, Mokwa-Bokani-Tegina da Minna-Tegina-Kontagora.

A kwanakin baya ma gwamnatin Jihar Neja ta karbe aikin titin Kontagora zuwa Rijau daga hannun gwamnatin tarayya, saboda dan kwangilar ya yi watsi da aikin hanyar na tsawon shekaru da dama.

Haka zalika, titin Minna-Sarikin Pawa da gwamnatin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ta fara, an yi watsi da shi tsawon shekaru 20, yayin da ba a tabbatar ko an bayar da kwangilar aikin titin Mokwa-New Bussa, wanda yanzu ya lalace ba.

A Jihar Filato, titin Jos-Akwanga, Bauchi zuwa Gombe, da Panbegwa a Jihar Kaduna da ke bi ta hanyar Saminaka zuwa Jingir da Bom Manchok, da dai sauransu, titunan gwamnatin tarayya ne da aka dade da yin watsi da su, kuma suna bukatar dauki cikin gaggawa.

Bayan haka, hanyar dajin Hawan-Kibo zuwa Jos, duk da cewa ta samu wasu tsaiko a bara, amma akwai bukatar a kara hada karfi da karfe wajen gyarata, domin ita ce babbar hanyar da ta hada yankin arewa maso gabashin Nijeriya.

A halin yanzu, wadannan hanyoyi sun zama tarkon mutuwa ga matafiya, wanda suka kasance sassanin ‘yan fashi da makami da masu garkuwa da mutane, wadanda suka yi wa titunan kawanya, suna jiran masu ababen hawa da ba su ji ba gani su kai musu farmaki.

LEADERSHIP ta gano cewa an bai wa wasu kamfanonin gine-gine hudu kwangilar gyaran wadannan hanyoyi a watan Maris na 2020.

Binciken da wakilinmu ya gudanar ya kuma nuna cewa ’yan kwangilar da ke gudanar da aikin gyaran wadannan hanyoyi sun bar wuraren, kuma masu ababen hawa na ci gaba da kokawa dangane da rashin kyawun hanyoyin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiTitinaTsayawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Barazanar Zanga-Zangar Kuncin Rayuwa Ta Girgiza Nijeriya

Next Post

Yadda Allah Yake Nuna Tausayi Da Girmama Manzon Allah S.A.W (1)

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

22 minutes ago
Hanyoyi
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

52 minutes ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

2 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

5 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

8 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

8 hours ago
Next Post
Yadda Allah Yake Nuna Tausayi Da Girmama Manzon Allah S.A.W (1)

Yadda Allah Yake Nuna Tausayi Da Girmama Manzon Allah S.A.W (1)

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Hanyoyi

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.