ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Hanyoyin Gwamnatin Tarayya Da Aka Yi Watsi Da Su A Jihohin Arewa 14

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Hanyoyi

Masu ababen hawa da mazauna jihohin Arewa 14 da aka yi watsi da ayyukan hanyoyin gwamnatin tarayya a jihohinsu sun yi kira ga Shugaban kasa Bola Tinubu da ministan ayyuka, Injiniya Dabid Umahi, kan halin da suke ciki na kunci bisa tabarbarewar hanyoyin gwamnatin tarayya.

Wani bincike da LEADERSHIP ta gudanar a jihohin Arewa 19 ya nuna cewa an bayar da kwangilar ayyukan manyan tituna da aka yi watsi da su tun bayan gwamnatin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo.

  • Munafurci Dodo Ne Me Shi Ya Kan Ci
  • Gwamnan Zamfara Ya Biya ‘Yan Fansho Hakkokinsu Fiye Da Nb7

Wasu kuma an yi watsi da ayyukan manyan titunan ne tun shekaru 10 da suka gabata na gwamnatocin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan da wanda ya gaje shi, Muhammadu Buhari.

ADVERTISEMENT

Sai dai Jihar Borno, wadda har zuwa lokacin hada wannan rahoto a daren jiya ba a samu kammala rahotonta ba, sauran jihohin da abin ya shafa an yi watsi da ayyukan tituna ne a tsakanin biyu zuwa 10.

Jihohi hudu da suka hada da Kaduna, Kebbi, Taraba, da Zamfara su ne mafi karancin hanyoyin da aka yi watsi da su, yayin da Jihar Kwara ke da mafi yawan ayyukan hanyoyin da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa a karkashin jagorancin Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

A Jihar Katsina kuwa, akwai kananan titunan gwamnatin tarayya da ke cikin mawuyacin hali, inda mafi yawansu ke bukatar gyara cikin gaggawa.

Titin Katsina zuwa Kano, wadda gwamnatin da ta shude ta bayar ba a kammala ba, ta tsaya a Gidan Mutun Daya.

Titin Mararaba Kankara zuwa Kankara a halin yanzu ana kan gyarawa, amma sauran muhimman hanyoyin ko dai an kasa gyarawa ko kuma ‘yan ta’adda sun mamayesu, wanda hakan ke kawo hadarurruka.

Titin Funtua zuwa Sheme dai ya shafe tsawon lokaci yana a lalace, lamarin da ya ta’azzara matsalar sace-sacen mutane da ake yi a yankin.

Haka zalika, titin Dutsinma zuwa Kankara, duk da cewa ana kulawa da shi sosai, ya zama yankin da ke fuskantar hadari saboda ‘yan fashin suna yi wa masu ababen hawa kwanton bauna tare da kai su dajin Rugu.

A Jihar Zamfara, babbar hanyar Jibiya zuwa Kaura Namoda, wacce a ake ganin hanya ce mai kyau da ta hada jihohin Katsina da Zamfara, amma a yanzu ta zama tarkon mutuwa saboda yawaitar ‘yan fashin daji.

A shekarar 2020, gwamnatin jihar ta ayyana shi a matsayin yankin da ba za a iya bi ba, tare da hana masu ababen hawa yin amfani da hanyar saboda yawaitar hare-haren ‘yan bindiga.

A Jihar Neja, kusan dukkan titunan gwamnatin tarayya sun lalace, wasu kuma gwamnatin jihar ta karbe su.

An shafe sama da shekaru 10 ana aikin titin Suleja zuwa Minna, wanda dan kwangilar ya yi watsi da shi tsawon shekaru uku, kafin ya koma aiki kimanin shekaru biyu da suka wuce. Ko da yake, binciken LEADERSHIP ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki nauyin gina sauran sassan hanyar da ta tashi daga Kakaki a karamar hukumar Paikoro zuwa Minna, babban birnin jihar, saboda tafiyar hawainiya da aikin hanyar yake yi.

Haka kuma bangaren Agaie-Bida na hanyar Lambata-Bida har yanzu yana cikin mummunan yanayi duk da cewa an bayar da kwangilolin hanyar kimanin shekaru biyar da suka gabata, haka ma hanyoyin Mokwa-Jebba, Mokwa-Bokani-Tegina da Minna-Tegina-Kontagora.

A kwanakin baya ma gwamnatin Jihar Neja ta karbe aikin titin Kontagora zuwa Rijau daga hannun gwamnatin tarayya, saboda dan kwangilar ya yi watsi da aikin hanyar na tsawon shekaru da dama.

Haka zalika, titin Minna-Sarikin Pawa da gwamnatin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ta fara, an yi watsi da shi tsawon shekaru 20, yayin da ba a tabbatar ko an bayar da kwangilar aikin titin Mokwa-New Bussa, wanda yanzu ya lalace ba.

A Jihar Filato, titin Jos-Akwanga, Bauchi zuwa Gombe, da Panbegwa a Jihar Kaduna da ke bi ta hanyar Saminaka zuwa Jingir da Bom Manchok, da dai sauransu, titunan gwamnatin tarayya ne da aka dade da yin watsi da su, kuma suna bukatar dauki cikin gaggawa.

Bayan haka, hanyar dajin Hawan-Kibo zuwa Jos, duk da cewa ta samu wasu tsaiko a bara, amma akwai bukatar a kara hada karfi da karfe wajen gyarata, domin ita ce babbar hanyar da ta hada yankin arewa maso gabashin Nijeriya.

A halin yanzu, wadannan hanyoyi sun zama tarkon mutuwa ga matafiya, wanda suka kasance sassanin ‘yan fashi da makami da masu garkuwa da mutane, wadanda suka yi wa titunan kawanya, suna jiran masu ababen hawa da ba su ji ba gani su kai musu farmaki.

LEADERSHIP ta gano cewa an bai wa wasu kamfanonin gine-gine hudu kwangilar gyaran wadannan hanyoyi a watan Maris na 2020.

Binciken da wakilinmu ya gudanar ya kuma nuna cewa ’yan kwangilar da ke gudanar da aikin gyaran wadannan hanyoyi sun bar wuraren, kuma masu ababen hawa na ci gaba da kokawa dangane da rashin kyawun hanyoyin.

Hanyoyi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
Labarai

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
Next Post
Yadda Allah Yake Nuna Tausayi Da Girmama Manzon Allah S.A.W (1)

Yadda Allah Yake Nuna Tausayi Da Girmama Manzon Allah S.A.W (1)

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.