• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Dan Nijeriya Da Girgizar Kasar Turkiyya Ta Shafa – Jakada

by Sadiq
3 years ago
Turkiyya

Jakadan Nijeriya a Kasar Turkiyya Ismail Yusuf, ya ce babu wani dan Nijeriya da girgizar kasar ta shafa.

Yusuf ya bayyana haka ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) a ranar Talata.

  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja
  • Mun Tara Wa Dan Takarar Gwamnanmu Miliyan 511 A Kano – NNPP

A cewarsa, ofishin Jakadancin yana cikin shirin ko ta kwana domin sanin halin da duk wani dan Nijeriya ke ciki a kasar.

NAN ta ruwaito cewa a safiyar ranar 6 ga watan Fabrairu, girgizar kasa mai karfin mita 7.8 ta afku a wasu garuruwa a Kudu Maso Gabashin kasar Turkiyya.

Shugaba Recep Erdogan, ya ce girgizar kasar ita ce Iftila’i mafi muni da kasar ta fuskanta cikin shekaru 84.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025 Dakta Seidu Adebayo Bello

Yusuf, ya ce ana ci gaba da aikin ceto kuma babu wani rahoto da aka samu na asarar rayukan ‘yan Nijeriya da ke zaune a yankin da lamarin ya shafa har zuwa lokacin da yake zantawa da NAN.

“Da sanyin safiyar ranar Litinin da karfe 4:17 na safe agogon Turkiyya, girgizar kasa mai karfin mita 6.5 zuwa 7.8 ta afku a garuruwan Malatya, Sanliurfa, Osmaniye, Diyarbakir da Gaziantep.

“Ba mu da labarin kowane dan Nijeriya a cikin wadanda abin ya shafa ya zuwa yanzu.

“Wannan aiki ne da ke gudana. Muna yin iyakar abin da za mu iya. Muna kokarin shimfida aikin ceto da matakan kariya.”

Yusuf ya ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jajanta wa gwamnati da al’ummar Kasar Turkiyya, inda ya yi alkawarin ‘yan bai wa Nijeriya goyon baya da hadin kai.

Ya zuwa yanzu dai sama da mutane 3,400 ne suka mutu a girgizar kasar a Turkiyya, inda dubbai suka jikkata, yayin da ake ci gaba da aikin ceto.

Yayin da sama da mutane 2,000 kuma aka bayar da rahoton sun mutu a Siriya a sanadin girgizar kasar ta afku.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu
Manyan Labarai

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025 Dakta Seidu Adebayo Bello

October 25, 2025
Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Next Post
Wannan Farfajiya Ta Nuna Tushen Alakar Afirka Da Sin

Wannan Farfajiya Ta Nuna Tushen Alakar Afirka Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

October 25, 2025
Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025 Dakta Seidu Adebayo Bello

October 25, 2025
Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Mata Ne Ginshikin Ci-Gaban Al’umma – Gimbiyar Dange

Mata Ne Ginshikin Ci-Gaban Al’umma – Gimbiyar Dange

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.