ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Tara Wa Dan Takarar Gwamnanmu Miliyan 511 A Kano – NNPP

by Sadiq
3 years ago
NNPP

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta kaddamar da shirin tara kudade ga jama’a domin yakin neman zaben dan takarar gwamnanta na jihar, Abba Kabiru Yusuf wanda aka fi sani da “Abba Gida”.

A wajen taron liyafar cin abinci na musamman da jam’iyyar ta shirya domin samun tallafin kudi daga ‘ya’yan jam’iyyar, NNPP ta ce an samu sama da Naira miliyan 511, wanda kaso mafi tsoka ya fito ne daga dan majalisa mai wakiltar Tofa/Dawakin-Tofa/Rimin-Gado a zauren majalisar wakilai Tijjani Abdulkadir Jobe wanda ya bada gudunmawar Naira miliyan 50.

  • Duniya Ta Shiga Alhinin Mutuwar Sama Da Mutum 3,000 A Turkiyya Da Siriya
  • An Gurfanar Da ‘Yan Bangar Siyasa 10 A Gaban Kotu A Sakkwato 

Da yake jawabi a wajen liyafar, shugaban masu bayar da tallafi kuma tsohon mai taimaka wa shugaban kasa, Abdulrahman Kawu Sumaila ya bayyana cewa NNPP ta himmatu wajen fara yakin neman zabe da goyon bayan mambobin jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Tsohon dan majalisar wakilan, ya karyata zargin sayen kuri’u da magudin zabe sannan ya kara da cewa jama’a sun taru ne domin su bayar da nasu tallafin.

Sumaila ya kara da cewa ’yan jam’iyyar NNPP masu sadaukarwa ne saboda suna da akidar Kwankwasiyya da ba ta da kudi.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Ya kara da cewa NNPP ta shirya tsaf domin kwato Kano daga jam’iyyar APC mai mulki a zaben gwamna da za a yi a wata mai zuwa.

“Zabe na karatowa kuma NNPP ba ta buri face kwato Kano. Mun taru a matsayinmu na NNPP da iyalan Kwankwasiyya don tattara kayan aiki don yakin neman zaben gwamna,” in ji Sumaila.

“Yanzu, cikin kasa da sa’o’i uku, mun samu tallafin jama’a sama da Naira miliyan 500 kuma har yanzu muna ci gaba da karbar tallafin. Kamar yadda kuka sani ba ma cikin gwamnati don haka ba mu da wani gata da asusun gwamnati don haka ne muke bude wannan taron jama’a inda muka nemi tallafi.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf, ya yaba da goyon bayan mambobin da suka bayar da gudunmawarsu, inda ya ce NNPP ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen gudanar da ayyukan al’umma idan har aka zabe su.

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

'Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.