ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Tara Wa Dan Takarar Gwamnanmu Miliyan 511 A Kano – NNPP

by Sadiq
3 years ago
NNPP

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta kaddamar da shirin tara kudade ga jama’a domin yakin neman zaben dan takarar gwamnanta na jihar, Abba Kabiru Yusuf wanda aka fi sani da “Abba Gida”.

A wajen taron liyafar cin abinci na musamman da jam’iyyar ta shirya domin samun tallafin kudi daga ‘ya’yan jam’iyyar, NNPP ta ce an samu sama da Naira miliyan 511, wanda kaso mafi tsoka ya fito ne daga dan majalisa mai wakiltar Tofa/Dawakin-Tofa/Rimin-Gado a zauren majalisar wakilai Tijjani Abdulkadir Jobe wanda ya bada gudunmawar Naira miliyan 50.

  • Duniya Ta Shiga Alhinin Mutuwar Sama Da Mutum 3,000 A Turkiyya Da Siriya
  • An Gurfanar Da ‘Yan Bangar Siyasa 10 A Gaban Kotu A Sakkwato 

Da yake jawabi a wajen liyafar, shugaban masu bayar da tallafi kuma tsohon mai taimaka wa shugaban kasa, Abdulrahman Kawu Sumaila ya bayyana cewa NNPP ta himmatu wajen fara yakin neman zabe da goyon bayan mambobin jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Tsohon dan majalisar wakilan, ya karyata zargin sayen kuri’u da magudin zabe sannan ya kara da cewa jama’a sun taru ne domin su bayar da nasu tallafin.

Sumaila ya kara da cewa ’yan jam’iyyar NNPP masu sadaukarwa ne saboda suna da akidar Kwankwasiyya da ba ta da kudi.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Ya kara da cewa NNPP ta shirya tsaf domin kwato Kano daga jam’iyyar APC mai mulki a zaben gwamna da za a yi a wata mai zuwa.

“Zabe na karatowa kuma NNPP ba ta buri face kwato Kano. Mun taru a matsayinmu na NNPP da iyalan Kwankwasiyya don tattara kayan aiki don yakin neman zaben gwamna,” in ji Sumaila.

“Yanzu, cikin kasa da sa’o’i uku, mun samu tallafin jama’a sama da Naira miliyan 500 kuma har yanzu muna ci gaba da karbar tallafin. Kamar yadda kuka sani ba ma cikin gwamnati don haka ba mu da wani gata da asusun gwamnati don haka ne muke bude wannan taron jama’a inda muka nemi tallafi.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf, ya yaba da goyon bayan mambobin da suka bayar da gudunmawarsu, inda ya ce NNPP ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen gudanar da ayyukan al’umma idan har aka zabe su.

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

'Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.