• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Ya Isa Ya Alakanta Ni Da Satar Dukiyar Jama’a – Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce babu wanda zai alakanta shi da satar dukiyar jama’a a lokacin da yake kan mulki.

Buhari ya nuna cewa bai tara wata dukiya a boye ba, “Ba ni da ko taku daya na fili a kasar waje.”

  • An Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 3 A Arewacin Kamaru
  • Albishiri Ga Masu Son Kawo Ziyara Kasar Sin

Da yake magana a Damaturu, a Jihar Yobe a wajen liyafar da aka shirya domin karrama shi a daren ranar Litinin kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina, ya sanar cikin wata sanarwar da ya fitar, ya nanata rantsuwar da ya yi na cewa zai yi gaskiya har ranar da zai kammala wa’adinsa na mulki.

Ya shawarci ‘yan Nijeriya da su ci gaba da kasancewa masu kishin kasa, “Sama da shekara 30 ina fada, ba mu da wata kasa da ta wuce mana Nijeriya, ya kamata mu tsaya mu hada karfi da karfe mu ceto ta.’’

Shugaban ya nuna farin cikinsa kan yadda lamura ke kara dawowa daidai a jihohin Arewa Maso Gabas da suka sha fama da matsalar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

Ya ayyana cewar ya cika alkawarin da ya yi a lokacin da ya karbi mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2015 kan yaki da ‘yan Boko Haram da daidaita lamura a kasar nan.

‘‘A Arewa Maso Gabas, Allah ya taimake mu mun kawar da Boko Haram, tattalin arziki ya farfado.

“Wasu mutane na tambaya ta kan nasarorin da na cimma a bangaren alkawarin da na yi kan yaki da cin hanci da rashawa.

‘‘To, a karkashin wannan tsarin yaki da rashawa da cin hanci ba karamin abu ba ne. A lokacin da nake soja, shugaba a zamanin soja, na kulle wasu mutane saboda kundin tsarin mulki ya ce dole ka ayyana kadarorinka, mutanen da ba su bayyana na kulle su.

“A karshe dai ni ma an kulle ni. Don haka, idan kana son ka hidimta wa kasar nan dole ka shirya wa shan wahala. Amma akwai abu guda da nake gode wa Allah a kai, babu wani mutum da zai iya bakanta ni. Ba ni da ko takudin fili a wajen Nijeriya kuma ina da niyyar zama a Nijeriya ko da na yi ritaya daga hidimta wa al’umma.”

Buhari ya yi godiya ga ‘yan Nijeriya da suka fahimce shi domin a cewarsa ya yi rantsuwa zai yi aiki tsakanin da Allah da kishin kasa.

Buhari ya gode wa gwamna Mai Mala Buni bisa kokarin da ya yi kan matsalar tsaro da daidaita zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar tare da shimfida ayyukan raya kasa.

Shi ma a jawabinsa, gwamna Buni, ya gode wa Buhari bisa kaddamar da ayyuka a jihar da suka kunshi Yobe katafaren sashen filin jirgin sama, babbar kasuwar zamani ta Damaturu, sashen kula da mata masu juna biyu da yara a Asibitin Koyarwa na Jihar Yobe, rukunin gidaje 2600 a Potiskum da kuma babbar makarantan Damaturu a Bra-Bra.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
Next Post
Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.