• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Ya Isa Ya Alakanta Ni Da Satar Dukiyar Jama’a – Buhari

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babu Wanda Ya Isa Ya Alakanta Ni Da Satar Dukiyar Jama’a – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce babu wanda zai alakanta shi da satar dukiyar jama’a a lokacin da yake kan mulki.

Buhari ya nuna cewa bai tara wata dukiya a boye ba, “Ba ni da ko taku daya na fili a kasar waje.”

  • An Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 3 A Arewacin Kamaru
  • Albishiri Ga Masu Son Kawo Ziyara Kasar Sin

Da yake magana a Damaturu, a Jihar Yobe a wajen liyafar da aka shirya domin karrama shi a daren ranar Litinin kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina, ya sanar cikin wata sanarwar da ya fitar, ya nanata rantsuwar da ya yi na cewa zai yi gaskiya har ranar da zai kammala wa’adinsa na mulki.

Ya shawarci ‘yan Nijeriya da su ci gaba da kasancewa masu kishin kasa, “Sama da shekara 30 ina fada, ba mu da wata kasa da ta wuce mana Nijeriya, ya kamata mu tsaya mu hada karfi da karfe mu ceto ta.’’

Shugaban ya nuna farin cikinsa kan yadda lamura ke kara dawowa daidai a jihohin Arewa Maso Gabas da suka sha fama da matsalar tsaro.

Labarai Masu Nasaba

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

Ya ayyana cewar ya cika alkawarin da ya yi a lokacin da ya karbi mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2015 kan yaki da ‘yan Boko Haram da daidaita lamura a kasar nan.

‘‘A Arewa Maso Gabas, Allah ya taimake mu mun kawar da Boko Haram, tattalin arziki ya farfado.

“Wasu mutane na tambaya ta kan nasarorin da na cimma a bangaren alkawarin da na yi kan yaki da cin hanci da rashawa.

‘‘To, a karkashin wannan tsarin yaki da rashawa da cin hanci ba karamin abu ba ne. A lokacin da nake soja, shugaba a zamanin soja, na kulle wasu mutane saboda kundin tsarin mulki ya ce dole ka ayyana kadarorinka, mutanen da ba su bayyana na kulle su.

“A karshe dai ni ma an kulle ni. Don haka, idan kana son ka hidimta wa kasar nan dole ka shirya wa shan wahala. Amma akwai abu guda da nake gode wa Allah a kai, babu wani mutum da zai iya bakanta ni. Ba ni da ko takudin fili a wajen Nijeriya kuma ina da niyyar zama a Nijeriya ko da na yi ritaya daga hidimta wa al’umma.”

Buhari ya yi godiya ga ‘yan Nijeriya da suka fahimce shi domin a cewarsa ya yi rantsuwa zai yi aiki tsakanin da Allah da kishin kasa.

Buhari ya gode wa gwamna Mai Mala Buni bisa kokarin da ya yi kan matsalar tsaro da daidaita zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar tare da shimfida ayyukan raya kasa.

Shi ma a jawabinsa, gwamna Buni, ya gode wa Buhari bisa kaddamar da ayyuka a jihar da suka kunshi Yobe katafaren sashen filin jirgin sama, babbar kasuwar zamani ta Damaturu, sashen kula da mata masu juna biyu da yara a Asibitin Koyarwa na Jihar Yobe, rukunin gidaje 2600 a Potiskum da kuma babbar makarantan Damaturu a Bra-Bra.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaBoko HaramBuhariCin HanciMatsalar TsaroRashawaYola
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 3 A Arewacin Kamaru

Next Post

Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

Related

Sojoji
Manyan Labarai

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

37 minutes ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

3 hours ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

8 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

11 hours ago
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

1 day ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

1 day ago
Next Post
Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

June 25, 2025
Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

June 25, 2025
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

June 25, 2025
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.