• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Ya Isa Ya Alakanta Ni Da Satar Dukiyar Jama’a – Buhari

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babu Wanda Ya Isa Ya Alakanta Ni Da Satar Dukiyar Jama’a – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce babu wanda zai alakanta shi da satar dukiyar jama’a a lokacin da yake kan mulki.

Buhari ya nuna cewa bai tara wata dukiya a boye ba, “Ba ni da ko taku daya na fili a kasar waje.”

  • An Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 3 A Arewacin Kamaru
  • Albishiri Ga Masu Son Kawo Ziyara Kasar Sin

Da yake magana a Damaturu, a Jihar Yobe a wajen liyafar da aka shirya domin karrama shi a daren ranar Litinin kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina, ya sanar cikin wata sanarwar da ya fitar, ya nanata rantsuwar da ya yi na cewa zai yi gaskiya har ranar da zai kammala wa’adinsa na mulki.

Ya shawarci ‘yan Nijeriya da su ci gaba da kasancewa masu kishin kasa, “Sama da shekara 30 ina fada, ba mu da wata kasa da ta wuce mana Nijeriya, ya kamata mu tsaya mu hada karfi da karfe mu ceto ta.’’

Shugaban ya nuna farin cikinsa kan yadda lamura ke kara dawowa daidai a jihohin Arewa Maso Gabas da suka sha fama da matsalar tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Ya ayyana cewar ya cika alkawarin da ya yi a lokacin da ya karbi mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2015 kan yaki da ‘yan Boko Haram da daidaita lamura a kasar nan.

‘‘A Arewa Maso Gabas, Allah ya taimake mu mun kawar da Boko Haram, tattalin arziki ya farfado.

“Wasu mutane na tambaya ta kan nasarorin da na cimma a bangaren alkawarin da na yi kan yaki da cin hanci da rashawa.

‘‘To, a karkashin wannan tsarin yaki da rashawa da cin hanci ba karamin abu ba ne. A lokacin da nake soja, shugaba a zamanin soja, na kulle wasu mutane saboda kundin tsarin mulki ya ce dole ka ayyana kadarorinka, mutanen da ba su bayyana na kulle su.

“A karshe dai ni ma an kulle ni. Don haka, idan kana son ka hidimta wa kasar nan dole ka shirya wa shan wahala. Amma akwai abu guda da nake gode wa Allah a kai, babu wani mutum da zai iya bakanta ni. Ba ni da ko takudin fili a wajen Nijeriya kuma ina da niyyar zama a Nijeriya ko da na yi ritaya daga hidimta wa al’umma.”

Buhari ya yi godiya ga ‘yan Nijeriya da suka fahimce shi domin a cewarsa ya yi rantsuwa zai yi aiki tsakanin da Allah da kishin kasa.

Buhari ya gode wa gwamna Mai Mala Buni bisa kokarin da ya yi kan matsalar tsaro da daidaita zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar tare da shimfida ayyukan raya kasa.

Shi ma a jawabinsa, gwamna Buni, ya gode wa Buhari bisa kaddamar da ayyuka a jihar da suka kunshi Yobe katafaren sashen filin jirgin sama, babbar kasuwar zamani ta Damaturu, sashen kula da mata masu juna biyu da yara a Asibitin Koyarwa na Jihar Yobe, rukunin gidaje 2600 a Potiskum da kuma babbar makarantan Damaturu a Bra-Bra.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaBoko HaramBuhariCin HanciMatsalar TsaroRashawaYola
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 3 A Arewacin Kamaru

Next Post

Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

Related

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

3 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

10 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

14 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

1 day ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

1 day ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

2 days ago
Next Post
Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.