ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Ya Isa Ya Alakanta Ni Da Satar Dukiyar Jama’a – Buhari

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce babu wanda zai alakanta shi da satar dukiyar jama’a a lokacin da yake kan mulki.

Buhari ya nuna cewa bai tara wata dukiya a boye ba, “Ba ni da ko taku daya na fili a kasar waje.”

  • An Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 3 A Arewacin Kamaru
  • Albishiri Ga Masu Son Kawo Ziyara Kasar Sin

Da yake magana a Damaturu, a Jihar Yobe a wajen liyafar da aka shirya domin karrama shi a daren ranar Litinin kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina, ya sanar cikin wata sanarwar da ya fitar, ya nanata rantsuwar da ya yi na cewa zai yi gaskiya har ranar da zai kammala wa’adinsa na mulki.

ADVERTISEMENT

Ya shawarci ‘yan Nijeriya da su ci gaba da kasancewa masu kishin kasa, “Sama da shekara 30 ina fada, ba mu da wata kasa da ta wuce mana Nijeriya, ya kamata mu tsaya mu hada karfi da karfe mu ceto ta.’’

Shugaban ya nuna farin cikinsa kan yadda lamura ke kara dawowa daidai a jihohin Arewa Maso Gabas da suka sha fama da matsalar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Ya ayyana cewar ya cika alkawarin da ya yi a lokacin da ya karbi mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2015 kan yaki da ‘yan Boko Haram da daidaita lamura a kasar nan.

‘‘A Arewa Maso Gabas, Allah ya taimake mu mun kawar da Boko Haram, tattalin arziki ya farfado.

“Wasu mutane na tambaya ta kan nasarorin da na cimma a bangaren alkawarin da na yi kan yaki da cin hanci da rashawa.

‘‘To, a karkashin wannan tsarin yaki da rashawa da cin hanci ba karamin abu ba ne. A lokacin da nake soja, shugaba a zamanin soja, na kulle wasu mutane saboda kundin tsarin mulki ya ce dole ka ayyana kadarorinka, mutanen da ba su bayyana na kulle su.

“A karshe dai ni ma an kulle ni. Don haka, idan kana son ka hidimta wa kasar nan dole ka shirya wa shan wahala. Amma akwai abu guda da nake gode wa Allah a kai, babu wani mutum da zai iya bakanta ni. Ba ni da ko takudin fili a wajen Nijeriya kuma ina da niyyar zama a Nijeriya ko da na yi ritaya daga hidimta wa al’umma.”

Buhari ya yi godiya ga ‘yan Nijeriya da suka fahimce shi domin a cewarsa ya yi rantsuwa zai yi aiki tsakanin da Allah da kishin kasa.

Buhari ya gode wa gwamna Mai Mala Buni bisa kokarin da ya yi kan matsalar tsaro da daidaita zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar tare da shimfida ayyukan raya kasa.

Shi ma a jawabinsa, gwamna Buni, ya gode wa Buhari bisa kaddamar da ayyuka a jihar da suka kunshi Yobe katafaren sashen filin jirgin sama, babbar kasuwar zamani ta Damaturu, sashen kula da mata masu juna biyu da yara a Asibitin Koyarwa na Jihar Yobe, rukunin gidaje 2600 a Potiskum da kuma babbar makarantan Damaturu a Bra-Bra.

Buhari
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Next Post
Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.