ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Albishiri Ga Masu Son Kawo Ziyara Kasar Sin

by CMG Hausa
4 years ago
Kasar Sin

Abokaina, albishirin ku, Ina fatan za ku ce GORO. Madalla. Ku karkade kunnuwanku… sanin kowa ne cewa, kasar Sin ta gyara manufarta ta kandaganrkin yaduwar cutar COVID-19 a kwanan baya, wadda ta kunshi daidaita ka’idojin shigi da fici. Tun daga ranar 8 ga watan da muke ciki, duk masu son shigowa Sin daga kasar waje, zai yi gwajin cutar COIVD-19 sa’o’i 48 kafin ya bar kasarsa, daga baya idan ya samu sakamakon ba ya dauke da cutar, to zai iya shiga kasar Sin kai tsaye, sa’an nan babu bukatar killacewa bayan ya shiga kasar.

Cikin shekaru 3 da suka wuce, yayin da annobar COVID-19 ke addabar al’ummar duniya, gwamnatin kasar Sin ta tsaurara matakan kandagarkin yaduwar cutar a bangaren shigi da fici, bisa manufarta ta dora matukar muhimmanci kan rayukan jama’a, da yin la’akari da hakikanin yanayin da kasar ke ciki a fannin dakile annobar. Matakan da suka hada da yi wa mutanen da suka shigo kasar Sin gwaji na COVID-19 bayan sun iso, da killacewa don magance yaduwar cutar, da dai sauransu. Wadannan matakai sun taka muhimmiyar rawa a kokarin kasar na dakile cutar COVID-19, duk da haka suna da nasu illar, wato matakan sun haifar da shinge ga cudanyar al’ummar Sinawa da na ragowar kasashen waje.

Sai dai a halin yanzu saboda raguwar karfin illar da kwayoyin cutar COVID-19 ke haifarwa, kana fiye da kashi 90% na al’ummar kasar Sin sun karbi cikakkun alluran rigakafin cutar, yayin da kasar ita ma ta samu ci gaba sosai a fannin kirkiro magunguna da adana isashen kayayyakin da ake bukata don jinyar mutanen da suka kamu da cutar COVID, suka sa kasar Sin samun damar daidaita manufarta ta dakile annoba, tare da saukaka matakan shigi da fici.

ADVERTISEMENT

Cikin shekarun 3 da suka wuce, wasu abokaina dake Najeriya da Nijar su kan tambaye ni, “Yaushe kasar Sin za ta saukaka matakanta na shiga kasar?” ko kuma “Zuwa yaushe zan iya zuwa kasar Sin don sayen kayayyaki?” kasancewarsu ‘yan kasuwa, wadanda suka saba zuwa biranen kasar Sin irinsu Guangzhou da Yiwu don sayen kayayyakin da suke bukata, kana kafin barkewar annobar COVID su kan ziyarci kasar Sin sau 3 zuwa 4 a shekara. Sai dai cutar COVID-19 ta sa shiga kasar Sin zama wani aiki mai wuya, don haka sun fara karkata ga yanar gizo ta Internet don sayen kayayyaki. Amma yin ciniki ta yanar gizo shi ma yana da wuya. Kamar yadda wani abokina dan kasuwa ya fada, “ Sai an buga waya kusan sau fiye da goma, da aike da sakonnin E-mail fiye da dari, kuma hakan bai kai yadda za a yi magana gaba cikin ‘yan mintuna ba.” Masu iya magana na cewa, zuwa da kai, ya fi aike. Ban da wannan kuma yadda aka dakatar da zirga-zirgar jiragen sama sakamakon samun fasinjoji da suka kamu da COVID a kai a kai, da hauhawar farashin hidimar jigilar kayayyaki, dukkansu sun haifar ma ‘yan kasuwan da matsaloli.

Ko da yake cinikin kasa da kasa a wadannan shekaru ya gamu da matsala, kana tattalin arzikin duniya na ci gaba da tafiyar hawainiya, amma cinikin da ake yi tsakanin Sin da Afirka na ta samun karuwa. Ko a watanni 6 na farko na shekarar 2022 kadai ma, darajar cinikayya a tsakanin Sin da Afirka ta kai dalar Amurka biliyan 137.4, jimillar da ta karu da kashi 16.6% idan an kwatanta da ta makamancin lokacin shekarar 2021. Inda darajar kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga kasashen Afirka ta kai dalar Amurka biliyan 60.6, adadin da ya karu da kashi 19.1% bisa na makamancin lokacin shekarar 2021. Duk wadannan karuwa an same su ne a wani lokacin da ake fuskantar matsala a fannin shigi da fici na kasar Sin. Saboda haka, ana iya kyautata zaton cewa, bayan da aka saukaka matakan kayyade shigi da fici, ‘yan kasuwan kasashen Afirka da na kasar Sin za su samu damar gudanar da karin ziyarar aiki, da cudanya da juna fuska da fuska, lamarin da zai sanya adadin cinikin Sin da Afirka karuwa sosai.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Wannan karuwar cinikayyar za kuma ta sa kasashen Afirka samun karin kudin shiga a fannin harajin kwastam, da kudin da ‘yan kasashen suke aikewa gida, ta yadda hakan zai saukaka matsin lamba ga tattalin arziki. Haka zalika, karuwar ciniki za ta sanya kudin da ake kashewa a fannonin jigilar kayayyaki da adana su ya ragu, ta yadda ‘yan kasuwan kasashen Afirka za su samu karin riba, kana jama’ar kasashe daban daban dake nahiyar Afirka su ma za su samu damar samun kayayyaki masu araha da inganci. Ban da wannan kuma, kamar yadda kasar Kenya ta fara sayar da ’ya’yan marmari na Avocado zuwa kasar Sin a watan Agustan bara, karin kayayyakin kirar kasashen Afirka za su samu damar shiga cikin kasuwannin kasar Sin, don baiwa kasashen da suke samar da su riba da karin guraben aikin yi.

Ba shakka amfanin daidaita matakai masu alaka da shigi da fici bai tsaya ga bangaren ciniki kawai ba, ganin yadda farfadowar cudanyar mutanen kasashen Afirka da na kasar Sin za ta haifar da ci gaban harkokin zuba jari, da yawon shakatawa, da al’adu, da aikin samar da ilimi, da dai sauransu. Yadda kasar Sin ta daidaita manufarta a fannonin kandagarkin cutar da aikin mai alaka da shigi da fici, ta nuna wa kasashen duniya cewa, “An yi ban kwana da lokaci mai wahalar gaske, yanzu lokaci ya yi da ya kamata a hada hannu don samun cikakkiyar farfadowa daga illar da annobar COVID-19 ta haifarwa duniyar bil-Adama.” (Bello Wang)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
INEC Ta Fitar Da Sabbin Ka’idojin Zaben 2023

2023: INEC Ta Musanta Sake Fitar Da Sunayen 'Yan Takara

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.