• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana

by Hussein Yero
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Masu iya magana na cewa,abin da ya ci Doma bai barin Awai: Harin da ‘yan Bindiga suka kai gami da sace mutane a yankin Masarautar Dan Sadau, sakamakon kin biyan kudin fansa Naira miliyan 120, na kada hantar mutanan sauran kauyukan a koda yaushe sakamakon kin biyan nasu kudin.

Kauyukan da aka sanya wa kudin fansar aikin gona suna da dama amma,a Kananan Hukumomin Maru, Shinkafa, Anka, Maradun,Tsafe da Kauran Namoda abin ya fi tsanani.

  • Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024
  • Basirar Henry Kissinger Abu Mai Daraja Ne Ga Amurka

Domin ko a yanzu haka ‘yan Bindiga su kai hari a garin Ruwan Dorawa a mako biyu da suka wuce, inda suka sace mutum 13, da kisan mutum daya, sai kuma a ranar Juma’ar da ta gabata suka shiga yankin Masarautar Dan Sadau su kai sace mutum sama 100 a cikin daren wayewar gari Asabar da ta gabata.

Halin da da mutane Kauyukan, Mutunji, Kwanar Dutsi, Sabon Garin Mahuta da Unguwar Kawo, suke ciki baya ga sace mutanensu sama da 150 da ‘yan Bindigar suka yi karkashin jagorancin shugaban ‘yan Bindiga na Yanki Masarautar Dan Sadau Damuna.

Ya zuwa yanzu dai sama da mutane da dama ne  suka dawo gidajansu sakamakon lokacin da ‘yan Bindiga suke tafiya da su suka fashe suka fantsama cikin daji.

Wannan ne ya yi sanadiyyar dawowar mutane da dama bayan kwana biyu da kai masu harin, amma har yanzu wasu na hannunsu wadanda ba a san adadin su ba.

Daya daga cikin wadanda ya kubuta daga hannun ‘yan bindigar da ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana wa wakilinmu cewa, “A lokacin da ‘yan bindiga suka kora mu daji cikin dare da yake mun san yadda dajin yake da inda Dawa ke shuke da ciyayi masu tsawon duk inda aka a zo mutum ya san wurin sai ya sabe a guje ta haka ne mafi yawanmu muka tsira a hannun ‘yan Bindiga.”

“Ya kum tabbatar mana da cewa, shin Damuna zai sake dawowa garuruwan kuma lallai ba za su ji da dadiba.

Ana haka a ranar Lahadi sai ga motocin sojoji sun shigo garin amma zuwa Liitin sun bar garin, wannan ya kara sanya mana fargaba rashin sojoji a gari. Wannan ne ya sa yanzu haka wasu ke niyyar barin garin tun da ‘yan Bindiga sun tabbatar da cewa za su dawo kuma babu wani jami’in tsaro a garin.

A ta bangaren Gwamnatin Jihar Zamfara kuwa, ta bakin Gwamna Dauda Lawal da ya samu wakilcin, Shugaban Ma’aikata na Gidan Gwamnati, Muktat Muhammad Luga ya bayyana cewa, gwamnatin na sane da abubuwan rashin jindadi dake faruwa na tsaro a sasan jihar, gwamnatin na iyaka kokarinta don shawo kan matsalar tsaron.

Don yanzu haka ana ba wa ‘yan Sa kai horo domin tunkarar ‘yan Bindiga a duk inda suke a fadin Jihar.

Bangaren jama’an tsaro kuwa, Kakakin rundunar ‘yansandan na Jihar Zamfara, ASP Yazidu Abubakar ya bayyana wa manema labarai cewa, Rundunar Sojoji ne ke kula ya yankin Dan Sadau inda aka sace mutane sama mutum 100, sune ya kamata mu tuntuba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaka Mai Wuyar Da Masu Gidajen Burodi Ke Ciki A Kaduna – Yarima

Next Post

Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.