ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binani Ta Shigar Da Kara Kotu Kan Bukatar Ayyana Ta A Matsayin Wadda Ta Lashe Zabe

by Sadiq
3 years ago
Binani

‘Yar takarar gwamna a Jihar Adamawa a jam’iyyar APC, Sanata Aisha Binani Dahiru, ta shigar da kara a kotun tarayya da ke Abuja, inda ta nemi kotun ta yi nazari kan ayyanata da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) a matsayin wadda ta lashe zaben gwamna da aka karasa a ranar 16 ga watan Afirilu.

Binani ta kuma bukaci kotun da ta dakatar da INEC da wakilanta daga daukar mataki na gaba kan ayyana wanda ya lashe zaben, har sai kotun ta kammala yin nazari kan bukatar da ta shigar a gabanta.

  • Gwamnan Filato Ya Bukaci Jami’an Tsaro Su Kamo Wadanda Suka Kai Hari Wasu Yankunan Jihar
  • An Sace Ma’aurata Yayin Da Suke Dawowa Daga Coci A Osun

Binani ta ce hakan ya shafi doka ta 34 daya A da doka 31 a cikin baka da doka 3 2 a cikin baka a, b, c, da doka ta 6 ta babbar kotun tarayya ta shekarar 2019 da kuma ta sashe 251 1 a cikin baka q da kuma ta r kundin tsarin mulki na shekarar 1999 da ta sashe 149 da kuma ta sashe 152 ta dokar zabe ta shekarar 2022 da aka sabunta.

ADVERTISEMENT

Hujjojin karar da Binani ta shigar a gaban kotun ta bayyana cewa, bayan INEC ta tattaro sakamakon zaben, inda ta shigar da karar INEC a matsayin wadda ta ke kara ta farko wadda kuma ta ayyana ta a matsayin wadda ta lashe zaben, amma PDP da dan takarar ta gwamna Ahmadu Fintiri wanda ta shigar da kara a matsayin wanda ta ke kara na biyu da uku, sun fara tayar da rikici a jihar, inda hakan ya janyo dukan ma’aikatan INEC da cin zarafinsu.

A cewarta, tayar da rikicin ne ya janyo INEC ta soke ainahin sanar da sakamakon wadda alhali, ba ta karfin ikon yin hakan inda kotun sauraron karararkin zabe ce kawai keda wannan ikon.

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Ta ce, soke ayyana ta a matsayin wadda ta lashe zaben, hakan nuna cewa, INEC ta shiga cikin hurumin ikon kotun sauraron koke zabuka.

Ta gabatar da karar ce ta hanyar Lauyoyinta da babban lauya Hussaini Zakariyau ke jagoranta don kotun ta yi nazari kan ayyanata a matsayin wadda ta lashe zaben.

A cikin takardar bukatar ta Sanatan ta ce, kotu ce kadai keda hurumin daukar mataki kan jami’in INEC ba wai ita INEC din da kanta ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: APC Ta Kori Goje Daga Jam’iyyar Kan Zargin Yi Mata Zagon Kasa

Da Dumi-Dumi: APC Ta Kori Goje Daga Jam'iyyar Kan Zargin Yi Mata Zagon Kasa

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.