ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: APC Ta Kori Goje Daga Jam’iyyar Kan Zargin Yi Mata Zagon Kasa

by Sadiq
3 years ago
APC

Shugabannin jam’iyyar APC na gundumar Kashere da ke karamar hukumar Akko a Jihar Gombe, sun kori Sanata mai wakiltar Gombe ta tsakiya, Danjuma Goje, bisa zargin yi mata zagon kasa.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a kwanakin baya ne jam’iyyar a matakin Kashere ta kafa wani kwamiti da zai binciki zargin cin mutuncin jam’iyyar da tsohon gwamnan jihar, a lokacin zaben 2023 da aka kammala.

  • Binani Ta Shigar Da Kara Kotu Kan Bukatar Ayyana Ta A Matsayin Wadda Ta Lashe Zabe
  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Direba A Ondo

Da yake jawabi ga manema labarai a garin Kashere, shugaban jam’iyyar APC na yankin, Tanimu Abdullahi, ya bayyana cewa jam’iyyar ta dauki matakin korar Goje baki daya ne bayan ta same shi da laifukan cin mutuncin jam’iyyar da rashin halartar taron yakin neman zaben jam’iyyar APC a Jihar Gombe wanda jam’iyyar ta kasa ta jagoranta.

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Sanata Abdullahi Adamu, ya kara da cewa, ana kuma zargin Sanatan da kauracewa duk wani rangadin yakin neman zaben jam’iyyar a shiyyarsa.

“Kwamitin ya kuma tattauna kan zargin da ake yi wa Goje na yi wa jam’iyyun adawa aiki da ‘yan takararsu da nufin kawo cikas ga nasarar jam’iyyar APC a Jihar Gombe da ma Nijeriya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

Ya kara da cewa, “Bayan goyon baya ga ‘yan takarar jam’iyyar adawa ta hanyar karbar dan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar NNPP da kuma dan takarar majalisar wakilai ta tarayya a jam’iyyar PDP Akko a gidansa tare da bayar da goyon baya ga jam’iyyarsa ta APC da sauran al’amura da dama.

Abdullahi ya ci gaba da cewa, wasu laifukan da Sanata Goje ya aikata sun hada da “kawo cikas ga gwamnatin APC a jihar da kuma daukar nauyin yakin neman zabe da nufin tunzura jama’a kan gwamnatin APC a jihar.

“Bayar da takamaiman umarni ga abokansa da jami’an tsaronsa da su ki yin aiki da manufar jam’iyyar APC a Jihar Gombe.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Next Post
Rarara Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Ake Masa

Rarara Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Ake Masa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.