• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bincike Ya Nuna Tarin Fuka Na Kashe Mutum 71,000 A Nijeriya Duk Shekara

by Sani Anwar and Sulaiman
1 month ago
Tarin fuka

Cutar tarin fuka (TB), na daya daga cikin cututtuka mafi muni da kuma dadewa a duniya, wadda take ci gaba da lakume rayukan dubun nan ‘yan Nijeriya a kowace shekara, duk da cewa; ana iya yin rigakafi, ana kuma warkewa.

 

A shekarar 2023 kadai, Nijeriya ta samu mutuwar mutum 71,000, wadanda ke dauke da wannan cuta ta tarin fuka, inda ta zama ta daya a Afirka, kuma ta shida a duniya cikin kasashen da ke fama da ita.

  • Tinubu Ya Umarci A Yi Bincike Kan Hatsarin Jirgin Kasa Daga Abuja Zuwa Kaduna
  • Yadda Aka Gudanar Da Bikin Ranar Hausa Ta Duniya A Kano

An samu sabbin wadanda suka kamu da wannan cuta ta TB, su kimanin 499,000 a 2023, wadanda ke wakiltar kusan kashi 20 cikin 100 na masu dauke da cutar a Afirka, sannan kuma kashi 18 cikin 100 na wadanda cutar ta kashe a nahiyar. Duk kuwa da cewa, ana samun magunguna da gwaje-gwaje na cutar kyauta a dukkanin fadin kasar, sannan akwai dubbai wadanda ba a auna su ba da kuma wadanda suka fara shan magani a makare, wannan na taimakawa wajen ci gaba da yaduwar cutar a tsakanin al’umma.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

Duk da yawan wadanda aka gano suna dauke da cutar, jami’an kiwon lafiya sun bayyana irin ci gaban da ake samu. Daraktan kula da lafiyar al’umma a ma’aikatar lafiya ta tarayya, Dakta Godwin Ntadom, ya bayyana cewa; Nijeriya ta samu sanarwar bullar cutar tarin fuka mafi yawa a 2024, inda ta gano sama da mutum 400,000 da ke dauke da cutar, kwatankwacin kashi 79 cikin 100 na masu jinyar.

 

Haka nan, akwai yara da dama wadanda ke dauke da cutar ta TB, amma ba a gano ba. Kazalika, yaran da aka gano suna dauke da cutar, yawansu ya karu daga 8,293 a 2018 zuwa 43,000 a 2024, in ji shi.

 

Duk da haka, Ntadom ya bayyana cewa; tarin fuka wanda ba ya jin magani, shi ne wanda ya fi illa. “Adadin yawan masu dauke da cutar da ba a gano ba, su ne ke ci gaba da yada ta”, in ji shi.

 

Domin cike gibin da ake samu, gwamnatin tarayya a kwanan nan ta kaddamar da sauye-sauyen ayyukan fasaha. Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya sanar da tura na’urorin gwaji (D-ray) na wayar hannu guda 400 a fadin jihohin Nijeriya 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja.

 

“Wadannan rukunin, wadanda kwararru a bangaren ke sarrafa su, suna ba mu damar gano alamun cututtukan tarin fukar da ba a gano ba,” in ji Pate.

 

Gwamnati ta kuma damar yin gwajin kwayoyin cikin sauri. Tsakanin 2012 zuwa 2024, yawan kwararrun injinan gwaje-gwajen da aka samu sun karu daga 32 zuwa 513. Haka zalika, adadin cibiyoyin kula da tarin fuka ya kusan ninki biyu daga 12,606 a 2019, zuwa kusan 23,000 a 2024, wanda ya mamaye sama da rabin dukkanin cibiyoyin kiwon lafiya a fadin kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Labarai

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Matatar dangote
Labarai

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Labarai

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Next Post
Marafa Ya Fice Daga APC, Ya Zargi Tinubu Da Watsi Da Zamfara

Marafa Ya Fice Daga APC, Ya Zargi Tinubu Da Watsi Da Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Tarin fuka

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.