• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bincike Ya Nuna Tarin Fuka Na Kashe Mutum 71,000 A Nijeriya Duk Shekara

by Sani Anwar and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Zartar Da Dokar Karya Farashin Magunguna 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cutar tarin fuka (TB), na daya daga cikin cututtuka mafi muni da kuma dadewa a duniya, wadda take ci gaba da lakume rayukan dubun nan ‘yan Nijeriya a kowace shekara, duk da cewa; ana iya yin rigakafi, ana kuma warkewa.

 

A shekarar 2023 kadai, Nijeriya ta samu mutuwar mutum 71,000, wadanda ke dauke da wannan cuta ta tarin fuka, inda ta zama ta daya a Afirka, kuma ta shida a duniya cikin kasashen da ke fama da ita.

  • Tinubu Ya Umarci A Yi Bincike Kan Hatsarin Jirgin Kasa Daga Abuja Zuwa Kaduna
  • Yadda Aka Gudanar Da Bikin Ranar Hausa Ta Duniya A Kano

An samu sabbin wadanda suka kamu da wannan cuta ta TB, su kimanin 499,000 a 2023, wadanda ke wakiltar kusan kashi 20 cikin 100 na masu dauke da cutar a Afirka, sannan kuma kashi 18 cikin 100 na wadanda cutar ta kashe a nahiyar. Duk kuwa da cewa, ana samun magunguna da gwaje-gwaje na cutar kyauta a dukkanin fadin kasar, sannan akwai dubbai wadanda ba a auna su ba da kuma wadanda suka fara shan magani a makare, wannan na taimakawa wajen ci gaba da yaduwar cutar a tsakanin al’umma.

 

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Duk da yawan wadanda aka gano suna dauke da cutar, jami’an kiwon lafiya sun bayyana irin ci gaban da ake samu. Daraktan kula da lafiyar al’umma a ma’aikatar lafiya ta tarayya, Dakta Godwin Ntadom, ya bayyana cewa; Nijeriya ta samu sanarwar bullar cutar tarin fuka mafi yawa a 2024, inda ta gano sama da mutum 400,000 da ke dauke da cutar, kwatankwacin kashi 79 cikin 100 na masu jinyar.

 

Haka nan, akwai yara da dama wadanda ke dauke da cutar ta TB, amma ba a gano ba. Kazalika, yaran da aka gano suna dauke da cutar, yawansu ya karu daga 8,293 a 2018 zuwa 43,000 a 2024, in ji shi.

 

Duk da haka, Ntadom ya bayyana cewa; tarin fuka wanda ba ya jin magani, shi ne wanda ya fi illa. “Adadin yawan masu dauke da cutar da ba a gano ba, su ne ke ci gaba da yada ta”, in ji shi.

 

Domin cike gibin da ake samu, gwamnatin tarayya a kwanan nan ta kaddamar da sauye-sauyen ayyukan fasaha. Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya sanar da tura na’urorin gwaji (D-ray) na wayar hannu guda 400 a fadin jihohin Nijeriya 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja.

 

“Wadannan rukunin, wadanda kwararru a bangaren ke sarrafa su, suna ba mu damar gano alamun cututtukan tarin fukar da ba a gano ba,” in ji Pate.

 

Gwamnati ta kuma damar yin gwajin kwayoyin cikin sauri. Tsakanin 2012 zuwa 2024, yawan kwararrun injinan gwaje-gwajen da aka samu sun karu daga 32 zuwa 513. Haka zalika, adadin cibiyoyin kula da tarin fuka ya kusan ninki biyu daga 12,606 a 2019, zuwa kusan 23,000 a 2024, wanda ya mamaye sama da rabin dukkanin cibiyoyin kiwon lafiya a fadin kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’umma Da Ƴan Bindiga Sun Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Katsina

Next Post

Marafa Ya Fice Daga APC, Ya Zargi Tinubu Da Watsi Da Zamfara

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

2 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

3 hours ago
Tarin fuka
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

4 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

6 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

7 hours ago
Tarin fuka
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

9 hours ago
Next Post
Marafa Ya Fice Daga APC, Ya Zargi Tinubu Da Watsi Da Zamfara

Marafa Ya Fice Daga APC, Ya Zargi Tinubu Da Watsi Da Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Tarin fuka

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.