• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bitar Aikin Hajjin 2024

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
in Sharhi
0
Hajjin 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aikin Hajjin 2024, ya ajiye tarihin da ba za a manta da shi ba a tarihin aikin hajjin da Nijeriya ta halarta a kasar Saudiyya ta fuskoki da dama sakamakon tsare-tsaren da Hukumar jin dadin alhazai ta kasa, NAHCON ta aiwatar.

 

NAHCON, a karkashin jagorancin Malam Jalal Ahmad Arabi ta samu nasarori da yabo daga mahajjata da masu sanya ido a harkokin aikin hajji bisa aiwatar da tsare-tsaren kwarewa da hukumar ke da shi a tarihinta. Sai dai ana cewa, Ubangiji ne kadai ya cika 100 bisa 100.

  • Sojoji Sun Lalata Matatun Mai 20 A Yankin Niger Delta
  • Yadda Mai Haihuwar Fari Za Ta Kula Da Kanta (2)

Kwararren masanin aikin Hajji, Ustaz Abubakar Siddeq Muhammad, a cikin sharhinsa mai suna “Mal. Jalal Ahmad Arabi a aikin Hajjin 2024 (2)” wanda Kamfanin jaridar LEADERSHIP ya buga, ya yaba da tsare-tsaren shirye-shiryen Arafah da ba a taba yin irinsa ba inda ya ce. “A karon farko cikin fiye da shekaru 20, an shirya tantunan Nijeriya tsaf, an baje shimfidar kafet da na’urorin sanyi,” in ji shi.

 

Labarai Masu Nasaba

Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa

Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

Bugu da kari, wani masanin ayyukan aikin hajji, ya yi sharhi da tsokaci game da nasarorin da Arabi ya samu a lokacin jagorancinsa a matsayin shugaban hukumar NAHCON, kamar yadda aka buga a: “https://www.hajjnews.com.ng/2024/12/nahcon-in-2024-year-of-achievements-challenges-and-renewal.html”

 

Duk da cewa, rayuwa ba matabbata ba ce, haka ma, mulki ko jagoranci, suna da lokaci da iyaka. An yanke wa’adinsa jagorancinsa saboda wasu dalilai na siyasa da zarge-zarge amma shugabancin Jalal Arabi a matsayin Shugaban Hukumar NAHCON ya ba da sakamako wanda ya kawo sauyi, wanda a halin yanzu ke tabbace cikin cikakken bayanin rahoton Hukumar na 2024, mai taken “2024: Shekarar Nasarori, Kalubale, da Sabuntawa”.

 

Shugaban kasa, Bola Tinubu ne ya amince da nadin Arabi a matsayin Shugaban Hukumar NAHCON a ranar 17 ga watan Oktoban 2023.

 

Daga cikin muhimman abubuwan da tarihi ba zai manta da ambaton sunan Arabi ba, sun haɗa da:

1. Samun Biza cikin sauki: Duk wani mahajjaci ya samu bizarsa ne kafin fara jigilar alhazai.

2. Ayyukan jigilar mahajjata zuwa Saudiyya: Sama da Alhazai 52,000 ne aka kwashe kafin ranar 9 ga watan Yunin 2024, kafin cikar wa’adin da Saudiyya ke bai wa kasashe na kammala jigilar alhazai. Kuma an kammala jigilar dawo da alhazai gida Nijeriya da kwanaki biyar saura.

3. Jin dadin Alhazai a Mina: An raba kayayyakin jin dadi kamar kayan zuwa bayan gida da karamar fankar hannu don maganin zafi.

4. Kula da kiwon Lafiya: An bayar da magunguna kyauta na cututtukan da ake saurin kamuwa kamar zazzabin cizon sauro da hawan jini, tare da tabbatar da kulawa da mahajjata cikin gaggawa akan lokaci.

 

Wadannan nasarori, da aka cimma duk da kalubalen tattalin arziki, sun nuna jajircewa da sadaukarwar NAHCON. Ƙoƙarin Jalal Arabi ya sami karɓuwa a duniya a lokacin da aka keɓe shi aka ba shi damar shiga wani ɓangare a Ka’aba mai tsarki wanda aka keɓe ga fitattun mutane a duniya.

 

A yayin da NAHCON ke ci gaba da samun nasarori, aikin Hajji na 2025 ya shirya tsaf don samun nasara tare da gudanar da aikin hajji cikin sauki ga mahajjatan Nijeriya. Irin wannan shine amfanin kafa tushe mai ƙarfi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Mata Ke Daukar Yara Don Taya Su Aikin Gida

Next Post

Muhimman Abubuwan Da Suka Faru A Masana’antar Fina-finan Nijeriya A Shekarar 2024

Related

Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa
Sharhi

Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa

1 year ago
Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula
Sharhi

Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

1 year ago
Next Post
Hajjin 2024

Muhimman Abubuwan Da Suka Faru A Masana’antar Fina-finan Nijeriya A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.