ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON

by Muhammad
6 months ago
NAHCON

Mai taimakawa shugaban Hukumar NAHCON a kafafen yada labarai, Ahmad Muazu, ya ce akwai wani lokaci da yin shiru ba ya amfanar da al’umma wanda hakan yana faruwa ne idan aka riƙa maimaita ƙarya har ta ga ana buƙatar neman gaskiyar lamari.

Kowace ma’aikata na da nata ƙalubale, wanda ita ma Hukumar Aikin Hajji ta ƙasa (NAHCON), na fuskantar nata rikicin a ɓangaren shugabanci, duk da cewa abu ne da aka saba gani. Bayan kammala aikin Hajjin 2025, an buɗe wani sabon inda daga bisani kamar yadda aka saba, kanun labarai suka fara fitowa kan rahotannin zarge-zarge a salo daban-daban.

Abin da aka sanar da jama’a a watannin da suka gabata ba wai ilimantar ko ankararwa irin na aikin jarida ba kan gaskiya, illa labaran soki burutsu da ƙanzon kurege daga wasu ‘yan jarida da aka ɗauki hayarsu domin lalata amincewar da ke tsakanin jama’a, da shugabancin Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON), musamman babban shugabanta Farfesa Abdullahi Saleh Usman. An ƙirƙiro tare da tsara labaran ne a salon da ya ɗauki hankali ba bisa tsarin aikin jarida na gaskiya ba sai domin ɓata suna da matsin lamar ganin an sauya shugabanci ta hanyar amfani da farfagandar aikin jarida.

ADVERTISEMENT

Ina rubuta wannan ne ba a matsayin mai kallo daga nesa ba, illa a matsayin wanda ke aiki a cikin hukumar tate da ganin yadda ake tafiyar da al’amura, kuma na fahimci nauyin aikin da aka ɗora mata tare da girmama hukuma da muhimmancin nauyin da take ɗauke da shi ga miliyoyin Alhazan Nijeriya.

Idan aka duba da kyau, tsarin ya bayyana sarai duba da yadda rahotannin suka dogaro da “majiyoyi” marasa tushe da ba su taɓa fitowa fili ba inda ake ambaton manyan jami’ai da ba za a iya tantance su ba tare da faɗo “masana” da ba su da cikakkiyar fahimta game da tsarin aiki da doka da kuma hulɗar diflomasiyya da ke tattare da gudanar da shiriya Hajji. Kowane labari yana fitowa ne a gaggauce amma babu wanda zai iya tsayawa idan an yi masa tambayoyin asali ya bayar da cikakkiyar amsa. Labarin ɗaya ne kullum, sai dai kalmomi ne kawai ake sauyawa ganin yadda a yau zai fito da taken “na musamman” ne, gobe kuma “binciken ƙwakwag”, washegari “tantance gaskiya” da dai sauransu wanda laƙabi kawai ake sauyawa, amma abun iri ɗaya ne.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Tuggar Ya Sabunta Harkokin Diflomasiyyar Nijeriya

Bitar Aikin Hajjin 2024

A aikin jarida na gaskiya, tantance bayanai na zuwa kafin wallafawa, domin wannan shi ne ginshiƙin sahihanci, kasancewar ba a ɗaukar ɓangaren da ake zargi a matsayin abin dogaro ba tare da jin ɗayan ɓangaren ba. Amma da yawa daga cikin waɗannan labaran suna dogaro da jimla ɗaya kacal da ke cewa “an yi ƙoƙarin jin ta bakin hukumar amma bai yiwu ba”, domin rufe gazawar neman ɗayan ɓangaren labari wanda hakan ba ƙwazo ba ne, illa son kai da aka shirya domin cimma wata manufa ta kashin kai.

Abin lura shi ne, manyan kafafen watsa labarai masu daraja da suna suna guje wa waɗannan zarge-zarge, inda editoci ke neman hujjoji da takardu da gaskiyar lamarin, wanda wannan kaɗai ya isa ya faɗakar da jama’a. Zarge-zargen da ba za su iya tsallake gwajin tantancewa ba, sukan koma dandamali marasa tsari da ƙa’ida domin wasa da hankali.

Ya dace a tambaya: wace manufa waɗannan labaran ke da su? Idan gyara ake nema, da an fara da hujjoji tabbatattu da nazarin manufofi ba tare da son rai ba, da shawarwari a bayyane. Amma abin da muke gani shi ne hayaniya ba tare da shaida ba da kuma gaggawa ba tare da tushe ba. Irin wannan aikin ba gyara ba ne sai dai wani yunƙurin nufin matsa lamba ko neman wata dama wanda idan hakan ta ci tura, sai a ƙara ɓullo da wata dabara.

Wannan dabara ba sabuwa ba ce, sai dai sari da ake zargi kafin a fara tattaunawa, sannan a yi amfani da ita kan muradin jama’a, na buƙatar sanin gaskiya amma waɗanda suka ƙirƙiro labaran sun yi ne kawai domin buƙatar kan su da abinda za su samu da zaran sun wallafa kuma ba sai an kawo hujja ba saboda hayaniya ce manufar.

Yayin da ake fara shirye-shiryen Hajjin 2026, tun kafin a fara sarrafa biza ko kammala kasafi, an riga an fara kitsa irin waɗannan labarai wanda wannan ba wai hasashe ba ne, tsantsar shiri ne da suka fara tun tuni.

Abin da waɗannan masu kitsa labaran ba su fahimta ba shi ne NAHCON ba hukuma ce mai rauni da ke rayuwa da jin-ƙai ko kanun labarai ba. Hukuma ce ta doka, wadda Dokar NAHCON ta 2006 ta kafa, tare da bayyanannen nauyi na yi wa Musulman Nijeriya hidima a tafiyar Hajji, wadda ita ce mafi girman ibada a rayuwarsu. Tana da manufa a fili: samar da ingantattun ayyuka ga Alhazai. Hukumar ta fuskanci matsin lamba a baya kuma ta yi nasara akan guguwar da ta fi wannan ƙarfi.

Jama’a sun cancanci tsabtatavven bayani ba mai rikitarwa ba, tare sanin bambanci tsakanin aikin jarida na sa ido kan gaskiya da kuma matsin lamba da aka ɓoye da sunan nuna damuwa. Bugu da ƙari hujja da tsari da kuma manufa ta gari su na da muhimmanci.

Ga jama’a, roƙona a bayyane yake kancewa a lura da tsari tare da nuna shakka kan labaran da suke cike da zargi amma babu hujja. Sa’an nan jama’a su kwatanta aikin gudanar da Hajji mai natsuwa da tsari, da hayaniyar kanun labarai masu tayar da hankali.

Game da waɗanda ke cin riba ta hanyar yayata labaran da suka karkatar daga gaskiya, mun fahimci dabarunsu kuma irin waɗannan dabaru ba su daɗewa, hasali ma gaskiya ba ta buƙatar hayaniya domin ta yi halinta.

Hukumar NAHCON, za ta ci gaba da aikinta kuma Shugaban Hukumar zai ci gaba da sauke nauyin da aka ɗora masa, tare da cikakken goyon bayan kwamishinoni da kwamitin gudanarwa, ba don basa karɓar suka ba, sai don ayyukansu suna kan tsarin doka kuma suna da manufa da nufin hidima ga al’umma.

NAHCON
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Ba a Tsawaita Ranar 31 Ga Oktoba Ba Ta Dawowar Jakadun Nijeriya Gida – Minista
Sharhi

Yadda Tuggar Ya Sabunta Harkokin Diflomasiyyar Nijeriya

April 9, 2026
NAHCON
Sharhi

Bitar Aikin Hajjin 2024

December 30, 2024
Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa
Sharhi

Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa

May 17, 2024
Next Post
Tinubu Ya Gana da Ƙungiyoyin Ƙwadago Da Gwamnoni Kan Shirin Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya

Tinubu Ya Gana da Ƙungiyoyin Ƙwadago Da Gwamnoni Kan Shirin Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.