ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwan Da Suka Faru A Masana’antar Fina-finan Nijeriya A Shekarar 2024

Daga:  Tinubu Ya Nada Ali Nuhu Shugaban Hukumar Fina-finai Ta Nijeriya 

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
2 years ago
Fina-finan Nijeriya

Ranar 12 ga watan Janairun shekara ta 2024 da muke ciki, Shugaba Bola Ahmed Tinubu; ya nada shahararren jarumin fina-finai na Kannywood, Ali Nuhu; a matsayin Shugaban Hukumar Shirya Fina-finai ta Nijeriya (Nigeria Film Cooperation).

An kafa wannan hukuma ta shirya fina-finan Nijeriya, a shekarar 1979; karkashin doka mai lamba 61 na kundin tsarin mulkin Nijeriya, wadda aka dorawa alhakin sarrafa fina-finan Nijeriya.

  • Yadda Mata Ke Daukar Yara Don Taya Su Aikin Gida
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Kaddamar Da Gangamin Sa Yara A Makaranta

Har ila yau, a takaice hukumar na aiki ne a matsayin cibiyar gwamnatin tarayya; wacce aka dorawa dukkanin wani alhakin ganin masana’antar ta tsayu da kafafunta tare da fitar da kyawawan halaye da al’adun ‘yan Nijeriya a idon duniya.

ADVERTISEMENT

Kazalika, Ma’aikatar Yada Labarai da Al’adu ta Tarayya ce ke kula da ita tare da ba ta dukkanin wani iko da take bukata, domin bunkasa al’adu ta hanyar Sinima a Nijeriya.

Ta hanyar ayyukanta, hukumar na bayar da gudummawa kwarai da gaske ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin al’umma, samar da fina-finai don amfanin gida da kuma fitar da su zuwa kasashen waje; na daga cikin muhimman ayyukan da wannan hukuma ke gudanarwa.

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

 

Mutuwar Mista Ibu

A ranar 2 ga watan Maris na shekarar 2024, aka wayi gari da labarin mutuwar daya daga cikin manyan jaruman fina-finan Nijeriya (Nollywood) Mista Ibu.

John Okafor Ikechukwu, wanda aka fi sani da Mista Ibu; ya shafe fiye da shekara 40 a masana’antar fina-finai ta Nollywood, inda ya zama guda daga cikin manyan dattijan masana’antar da ake girmamawa; kafin ciwon kafa ya yi sanadiyar mutuwarsa, bayan fama da jinya.

An haifi Mista Ibu ranar 17 ga watan Oktoban shekara ta 1961, a Karamar Hukumar Nkanu West da ke Jihar Enugu, wanda bayan kammala karatunsa; sai ya tsunduma cikin harkar wasan kwaikwayo a shekarar 1978, ya kuma samu shahara a fagen wasan kwaikwayon; musamman a bangaren nishadi a dukkanin bangarorin Nollywood da kuma Kannywood.

Mista Ibu, ya kamu da ciwon kafa da ta kai har ga yanke masa kafar guda daya, an kuma kwantar da shi a asibitin da ke Lekki na Jihar Legas; kafin mutursa a ranar 2 ga watan Maris.

 

Gwamnatin Kano Ta Gwangwaje Wasu Jaruman Masana’antar Kannywood Da Manyan Motoci 

Yayin da wasu ke fita daga tsagin Kwankwasiyya a Jihar Kano suna komawa tsagin APC ta hannun Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin (Maliya), wadanda suka jurewa tsayawa a jam’iyar ta NNPP; sun rabauta da samun kyaututtukan manyan motoci masu tsada da kuma kudade daga Gwamnatin jihar.

Babban mai taimakawa Gwamnan Jihar Kano, a kan harkokin nishadi; Malam Tijjani Gandu ya bayyana cewa, gwamnan ya yi matukar yabawa da irin gudunmawar da jaruman suka ba shi, a lokacin da yake yakin neman zabensa.

Wasu daga cikin jaruman Kannywood, sun samu kyautukan motoci daga wurin Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf; ta hannun babban mai taimaka masa a kan harkokin nishadi, Malam Tijjani Gandu; wannan na daga cikin manyan alheran da jaruman masana’antar ta Kannywood suka samu a wannan shekarar ta 2024, da muke bankwana da ita.

 

Mutuwar Saratu Gidado

Ranar 9 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2024 ne, masana’antar Kannywood; ta wayi gari da mummunan labarin mutuwar daya daga cikin manyan jarumanta mata a masana’antar, Hajiya Saratu Gidado da aka fi sani da Daso.

Labarin rasuwar ya karade gidajen rediyon Kano, inda lamarin ya motsa zukatan jama’ar jihar da ma kasa baki-daya. Marigayiyar ta kwanta da dare, amma Allah bai nufi ta wayi safiya ba,‘yan’uwanta sun ce; ta rasu ne a yayin barcinta na daren Talata, bayan ta ci abincin Sahur. Daso dai, fitacciyar jaruma ce a masana’antar fina-finan Hausa, wacce ta shafe fiye da shekaru 18 a masana’antar.

 

Adam Zango Ya Zama Darakta Janar Na Gidan Talabijin Kausain

Ranar 8 ga watan Oktoba, Gidan Talabijin Kausain; guda daga cikin rukunin kamfanonin Kausain, ya bayyana wasu sabbin nade-naden da ya yi; domin jagorantar kamfanin a bangarori da dama. A cikin sanarwar Kausain TB, ta bayyana cewa; ta nada fitaccen jarumin fina-finan Kannywood, kuma mawaki Adam A. Zango a matsayin Darakta Janar na gidan talabijin din.

Shugaban Kungiyar Kausain, Alhaji Nasir Idris; a wata sanarwa da bayar a Abuja ya bayyana cewa, nadin Adam Zango a matsayin Darakta Janar; ya fara aiki ne nan take, kazalika a cewar sanarwar; an amince da nadin ne yayin wani taron kwamitin gudanarwa na kamfanin da aka gudanar.

Nan take bayan wannan sanarwa, jarumi Adam Zango; kuma sabon Darakta Janar na Kausain TB, ya wallafa a shafinsa na Facebook; domin ‘yan’uwa da abokan arziki su taya shi murna kan wannan sabon mukami da ya samu. Daga cikin wadanda suka taya shi murna, akwai Shugaban Hukumar Fina-finai ta Nijeriya, Ali Nuhu Muhammad; wanda ya yi masa fatan alheri da addu’ar samun nasara.

 

Rahama Sadau Ta Samu Mukami A Gwamnatin Tinubu 

Har ila yau, a cikin wannan shekara ne gwamnatin tarayya ta nada jarumar Kannywood, Rahama Sadau; a matsayin daya daga cikin shugabannin kwamitin bunkasa tattalin arzikin kasa ta hanyar fasaha da basirar zamani.

Sadau, ta samu wannan matsayi ne; bayan wani zama da suka yi da Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima; tare da sauran manyan mutane a fadar gwamnati, inda aka tabbatar mata da wannan matsayi tare da sauran ‘yan kwamitin.

An dora wa kwamitin, mai suna ‘Inbestment In Digital And Creatibe Enterprise’, hakkin zakulo ‘yan Nijeriya masu fasaha; musamman matasa, domin habaka tattalin arzikin kasa ta hanyar fasaha da basirar zamani a wannan karni.

 

Mutuwar El-Mu’az Birniwa 

Ranar 5 ga watan Disambar wannan shekara ne, mawaki kuma mai shirya fina-finai a masana’antar Kannywood, Mu’azu Muhammad Birniwa, wanda aka fi sani da El-Mu’az Birniwa ya rasu a wani yanayi mai cike da ban tsoro, rahotanni sun tabbatar marigayin na daga cikin ‘yan’uwa da abokan arzikin da suka buga kwallon kafa, domin taya mawaki Auta Waziri; murnar auren da zai yi.

Bayan buga wasan ne, sai •ya nufi asibiti sakamakon rashin jin dadin jikinsa da ya ji, nan take aka kwantar da shi a asbitin; bayan dan wani lokaci ya ce ga garinku. Kafin rasuwar El-Mu’az, ya shahara a fagen wakokin fadakarwa da soyayya.

Fina-finan Nijeriya
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
Fina-finan Nijeriya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Ba Zan Yi Ƙasa A Gwiwa Ba Wajen Ceto Manchester City Ba – Guardiola

Ba Zan Yi Ƙasa A Gwiwa Ba Wajen Ceto Manchester City Ba - Guardiola

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.