ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Tsaron

Ko dan jariri da ke cikin mahaifiyarsa ya san irin alkaba’in da ke addabar duniya a halin yanzu ta fuskar tabarbarewar tsaro.

Tsoro da firgici na ci gaba da haifar da razani a tsakanin al’umma. An mayar da kwararar da jinin Bil’adama ba a bakin komi ba.

  • Kotu Ta Tsare Mutane 29 Masu Rajin Kafa Kasar Yarbawa A Oyo
  • Wata Kungiya Ta Shirya Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi 400,000 A Nijeriya

Ana kashe mata da kananan yara, haka nan tsofaffi da dattawa duk babu wanda ya tsira. Dokokin kiyaye kisan kare-dangi tamkar ba su aiki saboda munafurcin Turawan yamma. Wanda suke so shi ne da gaskiya komai zaluncinsa wanda ya zamo dan adawarsu kuwa shi ne tunku-uwar-laifi duk irin gaskiyarsa.

ADVERTISEMENT

Tauye ‘yancin kasashe masu cin gashin kansu ya yawaita, karfafa abokan hulda masu tayar da zaune tsaye a kasashen da suka ki bayar da kai bori ya hau ya zama ruwan dare game da duniya. Duk wadannan abubuwa an gan su a Zahiri sun faru a Iraki, Libiya, Benezuela da wasunsu da dama. Sai kuma rikicin cikin gida da ake rurawa da kusan yau a duniya kasashe daidai ne suka tsira daga makircin su Amurka kan haka.

Al’ummar duniya ta gaji da alkaba’in rashin tsaron da ake fama da shi, wanda wani lokaci mutumin da yake rayuwa a doron kasa musamman a yankunan da abin ya fi kamari yake burin ina ma shi ne a cikin kabari. Kazantacciyar zubar da jinin da ake yi a yankin Gaza tun daga watan Oktobar bara zuwa yau ya isa abin misali baya ga rikicin da ya zama kamar cin kwan makauniya irin na Somaliya ko Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, sannan ga wanda ake fama da shi a tsakanin Rasha da Ukraine. Tambayar da kowa ke yi ita ce, yaushe masu haddasa wannan husuma za su bar al’ummar duniya ta numfasa?

LABARAI MASU NASABA

Yadda Tuggar Ya Sabunta Harkokin Diflomasiyyar Nijeriya

Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON

Mai karatu, na ci karo da wata kwakkwarar amsa a yayin da na samu labarin shawarar da kasar Sin ta gabatar mai taken Yunkurin Tabbatar da Tsaron Duniya, wadda Shugaba Di Jinping ya ambata a jawabinsa na bude taron Dandalin Boao, ranar 21 ga watan Afrilun 2022.

Wannan shawara cikin hikima da basira tana nuna matsayin kasar Sin na neman samar da ingantaccen tsaro mai amfanarwa tare da wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

Kasar Sin ta ba da shawarar kafa sabuwar hanyar tsaro bisa manufar tabbatar da tsaro na bai daya, da zai zama cikakke bisa hadin gwiwa wanda zai dore tare da mutunta juna a matsayin babban ginshiki. Haka nan shawarar tana neman a samar da wani tsari da zai sanya rashin rarraba tsaro a matsayin muhimmiyar ka’ida, da sanya burin samar da al’umma mai cikakkiyar tsaro a gaba.

Karin wani abin sha’awa game da wannan shawarar ta Yunkurin Tabbatar da Tsaron Duniya da kasar Sin ta gabatar shi ne, yadda ta kawo maslaha da tattaunawa da hadin gwiwa a matsayin mafita a maimakon amfani da adawa ko kawance na taron dangi.

Alamu sun nuna wannan shawara za ta samu nasara bisa yadda kasashe fiye da 100 da kungiyoyin yanki da na kasa da kasa suka yi na’am da ita tare da shigar da ita cikin kundayen huldar da ke tsakaninsu da kasar Sin, inda hakan ya sa ta zama abu mai muhimmanci ga sha’anin tsaron duniya.

Wannan tsari da shawarar ta kawo ya sha bamban da irin na kasashen yamma kamar su Amurka da ya jefa mu cikin alkaba’in tashe-tashen hankulan da muke gani a duniya. A tsarin tsaron su Amurka, kansu kawai suka sani ba ruwansu da saura da yi wa abin tanadi na fitar hankali kamar yadda Amurka ta ware Dala biliyan 886 a kasafinta na 2024 a fannin soja kawai. Wannan adadi da ya karu da kimanin Dala biliyan 30 a kan na bara, ba a taba ganin irin sa a tarihin kasar ba.

Har ila yau, sun hana duniya zaman lafiya domin kare muradun kansu ta hanyar kirkiro da kawance na soji daban-daban masu rarraba kawunan kasashe da kakaba takunkumai na karya tattalin arziki da tauye hakkoki da muradun kasashe wadanda dokokin duniya suka halatta da kuma zama kanwa uwar gami na wargaza sha’anin tsaron kasashe kamar yadda muke gani a Palasdinu da Tekun Kudancin Sin da Yankin Koriya.

Wannan ya sa nake da yakinin shawarar tabbatar da tsaron duniya da kasar Sin ta gabatar za ta wanzar da adalcin da ake fatan gani da zai zama silar magance alkaba’in duniya da kawar da tarnakin bunkasa ci gaban tattalin arzikin kasashe.

Tsaron
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Ba a Tsawaita Ranar 31 Ga Oktoba Ba Ta Dawowar Jakadun Nijeriya Gida – Minista
Sharhi

Yadda Tuggar Ya Sabunta Harkokin Diflomasiyyar Nijeriya

April 9, 2026
Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON
Sharhi

Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON

December 17, 2025
Tsaron
Sharhi

Bitar Aikin Hajjin 2024

December 30, 2024
Next Post
Me Ke Sa Wasu Maza Rashin Tsafta?

Me Ke Sa Wasu Maza Rashin Tsafta?

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.