• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Rahotonni
0
Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon jiya ne, bayan cika shekara 44 da kafuwa aka sauya fasalin kamfanin albarkatun mai na NNPC zuwa cikakken kamfani mai zaman kansa. Ana fatan wannan tsarin zai kai ga gwamnatin tarayya ta tsame hannunta daga zuba kudi wajen tafiyar da harkokin kamfanin kamar yadda dokar kafa kamfanin ta samar a shekarar 1977.

Sabon kamfanin NNPC Ltd zai gudanar da ayyukansa ne a halin yanzu kamar yadda dokokin kafa kamfanonin Nijeriya ta samar a karkashin dokar ‘Company and Allied Matters Act (CAMA)’.

  • Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya
  • Hukumar Kwastom Ta Cafke Miyagun Kwayoyi Na Kimanin Biliyan N1.4 A Legas

A wannan tsarin, Ma’aikatar Albarkatun Mai da Ma’aikatar Kudi suke da mallakin jarin kamfanin gaba daya ana kuma sa ran a nan gaba za a bude hannun jarin kamfanin ga al’ummar kasar ta hanyar sayar da hannayen jarin.

Idan za a iya tunawa a ranar 16 ga watan Agusta 2021 ne Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sanya hannun a kan dokar alkinta albarkatun man fetur wanda ya samar da tabbatar da cefanar da kamfanin NNPC don ya zama kamfani mai zaman kanshi, ana sa ran kamfanin zai gudanar da ayyukansa ta hanyar neman riba ba tare da dogara da kudaden gwamnati ba, ana kuma bukatar ganin ribar da kamfanin ke samarwa ta amfanar da masu hannun jari, wanda daga nan ne kuma za a shirya ganin hannun jarin gwamnati ya zama kashi 20 a cikin dari sauran kuma ga al’umm.

Da wannan shirin da aka samar, za a cigaba da gudanar da NNPC ne kamar yadda ake tafiyar da takwarorionta a sassan duniya, kamar Aramco a kasar Saudi Arabia, Petronas a Malaysia da Petrobras na kasar Brazil.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

A shekarar 2020, Aramco ta zama daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya inda a ranar 11 ga watan Mayu kudin ribar da ta samu ya zarce na kamfanoni irin su Apple Inc. a na kuma fatan cewa, a ‘yan shekaru masu zuwa kamfanin NNPC zai zama kamar Aramco a wajen samar da kudaden shiga ga kasar nan.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, tabbas wannan mataki ne da ya dace, muna kuma fatan za a samu nasara irin yadda muka gani tattare da kamfanin samar da iskar gas ta NLNG inda ta samar da ribar Dala Biliyan 100 a matsayin kudin shiga a shekara, muna da tabbacin cewa, in har aka sake wa sabon NNPC mara zai iya samun irin wannan nasarar.

Yana da matukar muhimmanci a bar sabon kamfanin NNPC ya gudanar da harkokinsa ba tare da katsalandan ba don samun cikakiyar nasarar da ake bukata.

Ana sa ran kamfanin NNPC ya zamab abban kamfani nan da shekaru masu zuwa, mun yi imanin za ta iya zama cikin manyan kamfanonin da za a yi alfahari da su a duniya.

Yana kuma da matukarm uhimmnanci a ra’ayinmu, sabbin mahukuntan NNPC su gudanar da cikakken bincike tare da garanbawul ga ma’aikatan kamfanin.

Wannan na da muhimanci don toshe duk wata hanyar da ake barnar kudaden kasa wannan abin da aka yi ta zargin kamfanin ke nan a baya. Ya kamata sabin masu tafiyar da kamfanin su tabbatar da babu almundahana da cin hanci da rashawa tattare da tafiyar.

Ya kuma kamata a dauki kwararrun ‘yan Nijeriya daga kamfanonin mai na duniya don samar da canjin da ake bukata.

Babbar tambaya anan ita ce ya za a yi da tallafin mai wanda yake tatse dan tattalin arzikin kasar nan da yake a kan gargara. Gwamnatin tarayya ta kiyasta kashe Naira Tiriliyan 6.72 a kan tallafin man fetur a shekara mai zuwa wannan kudin da aka kiyasata ya zarce kudin da aka kashe a wannan shekarar na Naira Tiriliyan 2.53.

A ra’ayinmu wannan ba abin da za a amince da shi ba ne.

Masana sun yi imanin cewa, da wannan cefanar da NNPC da aka yi ba za ta rika zuba kudade a asusun gwamnatin tarayya ba, wanda hakan na nufin cewa, a yanzu babu kudaden da gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi za su rinkarabawa a tsakaninsu, amma tabbas za ta rika biyan dukkan hakoki na haraji da sauransu ga gwamnati.

A ra’ayinmu, wannan labari ne, mai kyau don zai tilastawa yawancin gwamnonin jihohi neman wasu hanyoyin samar da kudaden gudanar da harkokinsu ba tare da jiran kudi daga gwamnatin tarayya ba.

Mun dade muna kira a wannan shafin cewa, ya kamata gwamnoni su zama kamar shugabanin manyan kamfanoni ta hanyar nema wa jihohinsu kudaden shiga. Amma yanzu da a aka samu janyewar wadannan kudaden ya zama dole su nema kansu wasu hanyoyi na daban na neman kudaden shiga.

Abin takaici kuma shi ne a halin yanzu da ya kamata Nijeriya ta ribaci yadda farashin man fetur ke hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yakin Rasha da Yukiren amma abin ba haka yake ba, a kan haka muke kira ga sabbin mahukuntan NNPC su duba yadda Nijeriya za ta ci gajiyar irin wannan lamarin don amfanin al’umma.

Muna kara jinjina ga gwamnatin tarayya a kan wannan mataki da ta dauka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKamfanin Mai Fetur Na KasaMele KyariNNPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69

Next Post

DA DUMI-DUMI: ‘Yan Bindiga Sun Sace Wani Basaraken Gargajiya Da Wasu Mutum 3 A Ondo

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Wasu Mutum 2 Da Suka Sace A Wata Cocin Jihar Abiya 

DA DUMI-DUMI: 'Yan Bindiga Sun Sace Wani Basaraken Gargajiya Da Wasu Mutum 3 A Ondo

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.