ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DA DUMI-DUMI: ‘Yan Bindiga Sun Sace Wani Basaraken Gargajiya Da Wasu Mutum 3 A Ondo

by Muhammad
4 years ago
Da

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun yi garkuwa da wani basaraken gargajiya na unguwar Iku, mai suna Oniku na Iku a yankin Ikare Akoko a jihar Ondo, Cif Mukaila Bello.

Yankin Iku na Ikare ya shahara wajen karbar bakuncin mutanen da ke zuwa Dam din Awara da filin wasa na Ikare, da dai sauransu.

  • An Gano Sama Da Yara 50 Da Aka Sace A Wani Cocin Ondo
  • Mun Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari A Cocin Katolika Dake Ondo – Amotekun

Wata majiya ta ce, an sace basaraken tare da Mista Adeniran Adeyemo, Mista Bashiru Adekile da kuma Cif Gbafinro.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta samu labarin cewa an yi garkuwa da mutanen ne a yammacin ranar Alhamis a Ago Panu a titin Owo-Ikare, kan hanyarsu ta Akure zuwa Ikare.

An tabbatar da cewa maharan sun harbe direban motar, sauran kuma suna karbar magani a wani asibiti da ba a bayyana ba a garin Owo.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Har yanzu dai masu garkuwa da mutanen ba su tuntubi iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su ba har zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto, amma dangin daya daga cikin wadanda aka kashe ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Akure, babban birnin jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ondo, Funmilayo Odunlami, ya ce rundunar ta samu kiran waya da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Alhamis kan lamarin.

Odunlami ya ce lamarin ya faru ne a kusa da Ago Yeye, daura da titin Owo-Ikare a jihar, inda ya kara da cewa ana ci gaba da kokarin da rundunar tsaro ta hadin guiwa domin ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da cafke masu garkuwa da mutane.

Ta ce, “’yan bindigar sun harbi wata mota kirar Toyota Corolla mai lamba REG. NO. KAK 818 AE, a yayin da suke kan tafiya, harsashin ya doki direban a kai, sai motar ta tsaya, sauran mutanen da ke cikin su kusan 4 ne (ba a san ko su waye ba). ) an jefa su cikin daji yayin da aka watsar da direban.

“’Yan sandan sun kwato motar ne yayin da aka kai direban asibiti, direban motar a halin yanzu yana cikin koshin lafiya yayin da ‘yansanda da mafarauta da ’yan banga a yankin ke kutsawa dajin domin ceto wadanda abin ya shafa tare da kamo maharan. .”

Da
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Kungiyar NAOWA Ta Nemi Matan Sojoji Su Karfafa Wa Mazajensu Wurin Yaki Da Ta’addanci

Kungiyar NAOWA Ta Nemi Matan Sojoji Su Karfafa Wa Mazajensu Wurin Yaki Da Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.