• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS

by Bello Hamza
9 months ago
in Tattalin Arziki
0
CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sanar da sabbin ka’idoji na sarrafa hada-hadar kasuwancin ‘PoS’ a fadin kasar nan, inda ya ba da umarnin cewa duk wani ciniki na POS zai bi ta ta hanyar cibiyar hadakar hada-hadar bankuna wato NIBSS ko UPSL, wanda wannan zai karya ikon tsohon tsarin da ake a kai na sarrafa mu’amalar kudi.

A cikin wata sanarwa mai kwanan ranar 11 ga watan Satumba, 2024 zuwa ga duk masu ba da sabis na hada hadar kudi zuwa kan PTSA (Payment Terminal Serbice Aggregators), CBN ta umurce su da su fara daidaitawa tare da PTSAs sannan su kuma sanar da CBN a rubuce domin tabbatar da bin wannan doka a cikin kwanaki 30 daga kan kwanan watan wannan takarda.

  • Anya Barcelona Za Ta Iya Kai Bantenta Kuwa A Gasar Zakarun Turai Ta Bana?
  • Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

Domin cimma manufar bin diddigin hada-hadar kasuwancin kudade a Nijeriya, CBN a watan Agustan 2011, ya ba da lasisin PTSA ga NIBSS.

Biyo bayan damuwa game da bayar da damar lura da duk wani sha’anin kudi ta PoS ga cibiya guda ɗaya tal, a ranar 19 ga Afrilu, 2024, ta ba da lasisin PTSA na biyu zuwa ga UPSL (Unified Payment Serbices Limited).Kusan watanni biyar bayan da ta ba da lasisi ga UPSL, CBN ya ba da umarnin cewa masu wannan hulda su “sanya duk wata mu’amalar kudi dake gudana a PoS a wuraren kasuwanci imma a zahiri, ko a kan manhajar PoS na zahiri ko na badini, ta hanyar PSTA da suke da lasisi da CBN.”Sanarwar ta ci gaba da cewa, “ana bukatar PTSAs su aika da mu’amalar PoS zuwa ga kawai ma’aikatan da aka sahhalewar lura da tsarin hada hadar kudi, wanda masu sha’anin kudi suka ayyana kuma CBN ta ba su lasisi. Dole ne dukkan masu sarrafawa wadanda suke da lasisi a hada su da PTSAs, ta yadda za a bai wa masu hulda damar zabar wacce hanya da kuma PTSA za su yi amfani da su.“Duk cibiyar da ke lura da sha’anin kudi (PTSPs) dole ne su tabbatar da cewa an saita na’urorin PoS, manhajarsu da ayyukansu da kuma mu’amalar kudada ta hanyar PTSA, kamar yadda aka bada umurni. Duk PTSPs za su gabatar da bayani a kowanne wata ga CBN, suna mai bayyana adadin ‘yan kasuwa da wakilan da suke gudanar da aiki a karkashin su, tare da ayyukan PTSA da ake amfani da su wajen tafiyar da hada-hadar da ta dace.“Kowacce PTSA ana bukatar ya gabatar da kudaden da aka samu a kowanne wata ga CBN, tare da bayar da cikakkun bayanai game da duk wata hada-hadar da aka sarrafa ta hanyoyin sadarwar su. Ana sa ran gabatar da wannan bayani da aka ambata a sama ga Daraktan lura da sashen kula da tsarin biyan Kudi, kasa da kwanaki bakwai bayan karshen kowanne wata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNPOS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dubun Wani Dan Shekara 74 Da Ake Zargi Da Sace Tabarmi A Masallaci Ta Cika

Next Post

Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7

Related

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

3 weeks ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

4 weeks ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 months ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 months ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

2 months ago
Next Post
Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7

Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.