• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS

by Bello Hamza
12 months ago
in Tattalin Arziki
0
CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sanar da sabbin ka’idoji na sarrafa hada-hadar kasuwancin ‘PoS’ a fadin kasar nan, inda ya ba da umarnin cewa duk wani ciniki na POS zai bi ta ta hanyar cibiyar hadakar hada-hadar bankuna wato NIBSS ko UPSL, wanda wannan zai karya ikon tsohon tsarin da ake a kai na sarrafa mu’amalar kudi.

A cikin wata sanarwa mai kwanan ranar 11 ga watan Satumba, 2024 zuwa ga duk masu ba da sabis na hada hadar kudi zuwa kan PTSA (Payment Terminal Serbice Aggregators), CBN ta umurce su da su fara daidaitawa tare da PTSAs sannan su kuma sanar da CBN a rubuce domin tabbatar da bin wannan doka a cikin kwanaki 30 daga kan kwanan watan wannan takarda.

  • Anya Barcelona Za Ta Iya Kai Bantenta Kuwa A Gasar Zakarun Turai Ta Bana?
  • Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

Domin cimma manufar bin diddigin hada-hadar kasuwancin kudade a Nijeriya, CBN a watan Agustan 2011, ya ba da lasisin PTSA ga NIBSS.

Biyo bayan damuwa game da bayar da damar lura da duk wani sha’anin kudi ta PoS ga cibiya guda ɗaya tal, a ranar 19 ga Afrilu, 2024, ta ba da lasisin PTSA na biyu zuwa ga UPSL (Unified Payment Serbices Limited).Kusan watanni biyar bayan da ta ba da lasisi ga UPSL, CBN ya ba da umarnin cewa masu wannan hulda su “sanya duk wata mu’amalar kudi dake gudana a PoS a wuraren kasuwanci imma a zahiri, ko a kan manhajar PoS na zahiri ko na badini, ta hanyar PSTA da suke da lasisi da CBN.”Sanarwar ta ci gaba da cewa, “ana bukatar PTSAs su aika da mu’amalar PoS zuwa ga kawai ma’aikatan da aka sahhalewar lura da tsarin hada hadar kudi, wanda masu sha’anin kudi suka ayyana kuma CBN ta ba su lasisi. Dole ne dukkan masu sarrafawa wadanda suke da lasisi a hada su da PTSAs, ta yadda za a bai wa masu hulda damar zabar wacce hanya da kuma PTSA za su yi amfani da su.“Duk cibiyar da ke lura da sha’anin kudi (PTSPs) dole ne su tabbatar da cewa an saita na’urorin PoS, manhajarsu da ayyukansu da kuma mu’amalar kudada ta hanyar PTSA, kamar yadda aka bada umurni. Duk PTSPs za su gabatar da bayani a kowanne wata ga CBN, suna mai bayyana adadin ‘yan kasuwa da wakilan da suke gudanar da aiki a karkashin su, tare da ayyukan PTSA da ake amfani da su wajen tafiyar da hada-hadar da ta dace.“Kowacce PTSA ana bukatar ya gabatar da kudaden da aka samu a kowanne wata ga CBN, tare da bayar da cikakkun bayanai game da duk wata hada-hadar da aka sarrafa ta hanyoyin sadarwar su. Ana sa ran gabatar da wannan bayani da aka ambata a sama ga Daraktan lura da sashen kula da tsarin biyan Kudi, kasa da kwanaki bakwai bayan karshen kowanne wata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNPOS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dubun Wani Dan Shekara 74 Da Ake Zargi Da Sace Tabarmi A Masallaci Ta Cika

Next Post

Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7

Related

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

1 week ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

2 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

2 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

2 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

3 weeks ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

3 weeks ago
Next Post
Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7

Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.