• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Mai: Magani Mai Daci Ga Kashi 99 Cikin 100 Na ‘Yan Nijeriya

by Sulaiman
1 year ago
in Rahotonni
0
Cire Tallafin Mai: Magani Mai Daci Ga Kashi 99 Cikin 100 Na ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Janye tallafin man fetur da sabuwar gwamnatin dimokuradiyya ta yi a Nijeriya ya haifar da cece-kuce a bangarori daban-daban. Gwamnati ta yi ikirarin cewa cire tallafin ya zama dole don ta samu kudin da za ta habaka ababen more rayuwa, jin dadin rayuwar jama’a, da habakar tattalin arziki. Sai dai da yawa daga cikin ‘yan Nijeriya ba su gamsu da wannan hujja ba, domin suna ganin cire tallafin tamkar cin amanar alkawuran zabe ne da kuma nauyi ga talakawan da ke fama da wahala.

Cire tallafin man fetur ya haifar da hauhawar farashin man fetur zuwa sama da Naira 630 kan lita daya, hawan da ba a taba gani ba! Hakan ya yi tasiri matuka kan farashin kayayyaki da ayyuka, kamar sufuri, abinci, kudin makaranta, da kula da lafiya da dai sauransu. Yawan hauhawar farashin kayayyaki ya haura sama da kashi 27, mafi girman da aka taba samu.

  • Mutane 19,000 Sun Amfana Da Tallafin Fadama III A Zamfara
  • Cire Tallafin Fetur: Kano Za Ta Biya Ma’aikata Karin Albashin N20,000, ‘Yan Fansho N15,000.

Naira kuma ta fadi idan aka kwatanta da Dala, yayin da ake musayar kusan Naira 800 a hukumance tana ciniki sama da Naira 1,200 a kasuwar bayan fage, bambacin fiye da Naira 500. Wadannan abubuwa sun samar da karyewan karfin tattalin arzikin da tabarbarewan rayuwar ‘yan Nijeriya, musamman ma wadanda suka fi kowa rauni, masu dogaro da kai, da marasa aikin yi.

Har ila yau, cire tallafin man fetur ya haifar da tarzoma da zanga-zangar nuna rashin amincewa da yajin aiki wanda bai yi tasiri ba, yayin da ‘yan Nijeriya da dama ke nuna rashin gamsuwa da fushinsu da matakin da gwamnati ta dauka yayin da wasu kuma suka dauki hanyar ‘Sidon- look’. Kungiyoyin kwadago, kungiyoyin farar hula, da jam’iyyun adawa sun yi kira da a sauya manufar ko kuma a rage farashin mai, sun kuma bukaci a kara mafi karancin albashi, da sake duba kudin wutar lantarki, da kuma kawo karshen cin hanci da rashawa da rashin iya gudanar da ayyuka a bangaren man fetur da sauran su.

A daya hannun kuma, gwamnatin ta yi kira da a yi hakuri da fahimtar juna, inda ta ce manufar ita ce mafi alheri ga al’umma, kuma nan ba da dadewa ba za a ga amfanin ga kowa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Amma abin lura a nan shi ne ne, a bangaren kungiyoyin kwadago sun kasa kare hakkin ‘yan Nijeriya masu karamin karfi, masu dogaro da kai, marasa aikin yi, da ma’aikatan gwamnati na jihohi sai dai kawai sun tattauna da gwanati ne kan ma’aikatan gwamnatin tarayya da ke aiki, wadanda ‘yan tsiraru ne, wannan ya nuna yadda kungiyoyin kwadago ke da karancin hangen nesa.

Wani abin takaicin kuma shi ne a halin da ake ciki da wannan wahalhalun da al’ummar Nijeriya ke fuskanta, ‘yan majalisar kasa sun “tsinci dami a kala” idan kowannensu ya yi gaba da sabuwar mota kirar Toyota Landcruiser jeeps ta Naira miliyan 160, wanda wannan ba karamar wauta bace da dolonci na dan Nijeriya.

Cire tallafin man fetur dai batu ne mai sarkakiya da ya raba kan al’ummar kasar. A gefe guda, wasu manazarta da masana sun goyi bayan manufar, suna masu cewa tallafin ba shi da amfani, ba shi da inganci, kuma mai azurta wasu tsirarun ‘yan Nijeriya ne. Sun yi nuni da cewa tallafin yana jawo wa gwamnati asarar kusan Naira tiriliyan 1 a duk shekara, wanda za a iya kashewa a wasu sassa. Sun kuma yi ikrarin cewa tallafin ya fi amfanar masu hannu da shuni, domin masu hannu da shuni sun fi amfani da mai. Sun kuma tabbatar da cewa tallafin na karfafa fasakwauri, tarawa da karkatar da man fetur zuwa kasashen makwabta, inda farashin ya yi tsada.

Don haka suka bukaci gwamnati da ta yi tsayiwar daka kan matakin da ta dauka tare da aiwatar da wasu gyare-gyare domin dakile tasirin manufofin ga al’umma.

A daya gefen kuma, wasu masana da kungiyoyi da masu fafutuka ‘yancin kai sun yi adawa da manufar, suna masu cewa tallafin yarjejeniya ce ta zamantakewa da kuma hakki na mutane.

Sun yi hasashen cewa tallafin yana bayar da taimako da tallafi ga jama’a, wadanda tuni suke fuskantan kalubale da wahalhalu. Sun kuma nuna shakku kan lokaci da kuma yadda tsarin zai kasance, inda suka ce kamata ya yi gwamnati ta tuntubi jama’a tare da tafiyar da al’umma kafin ta dauki wannan tsattsauran mataki.

Sun kuma kalubalanci gwamnati da ta yi lissafin kudaden da aka tara daga tallafin da aka cire da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana a bangaren man fetur.

Cire tallafin man fetur wani abu ne mai daci ga kashi 99 cikin 100 na ‘yan Nijeriya, wadanda tuni suke fafutukar shawo kan tabarbarewar tattalin arziki da kalubalen tsaro. Manufar cire tallafin ta fallasa matsalolin da ke tatare da tattalin arzikin Nijeriya da kuma nuna rashin daidaiton tsarin tattalin arzikin Nijeriya, wanda ya dogara kacokan kan kudaden shiga da man fetur ke shigo da su daga waje.

Manufar kuma ta nuna cin amana da rashin amincewar da jama’a ke da ita akan gwamnati, wadda ta hau kan madafun iko ta silar kawo sauyi da fatan alheri.

Duk da hujjojin da magoya baya da masu suka suka gabatar suna da inganci.

A karshe, idan aka takaita dukkanin muhawarar, daga ina za’a samo kudaden da aka ce za su yi rara tun da shi kasafin kudin bara tashin farko rabinsa bashi ne aka ciwo, kuma shi ma kasafin kudin wannan shekaran wanda aka gabatar kwanan baya fiye da rabi bashi ne za’a ciwo. Shin raba kayan tallafi da motocin CNG (motocin safa safa masu amfani da iskar gas) shi ne za su zama mafita?

Wanna al’amari ya fi kama da wauta da shirme!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cire Tallafin feturMatatar man feturTagomashin cire tallafin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalibin Kasar Benin: Ina Da Burin Kai Fasahohin Aikin Noma Na Kasar Sin Zuwa Kasar Benin

Next Post

Tarihin Katsina Daga Karni Na Goma

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Tarihin Katsina Daga Karni Na Goma

Tarihin Katsina Daga Karni Na Goma

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.