• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 122 A Nijeriya -UNICEF

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 122 A Nijeriya -UNICEF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), ya ce zuwa yanzu cutar mashako ta kashe rayukan yara kanana 122 a Nijeriya. 

A wata sanarwa da wakiliyar UNICEF a Nijeriya, Dokta Cristian Munduate, ta fitar a ranar Juma’a, ta ce cutar ta shafi jihohi 27 a Nijeriya.

  • Majalisa Ta Ki Amincewa Da Shirin Tinubu Na Daukar Matakin Soji A Kan Nijar
  • Manchester United Ta Dauki Hujland Daga Atalanta

Kana ta ce, zuwa watan Yulin 2023, an samu wadanda suka kamu da cutar 3,850 yayin da aka tabbatar da mutum 1,387 sun kamu da cutar.

Sanarwar, ta ce cutar ta shafi jihohin Kano, Yobe, Katsina, Lagos, Birnin tarayya Abuja, Sakkwato da Zamfara, wanda cutar ta kama a tsakanin yara ‘yan shekara 2 zuwa 14.

A cewarta, abin damuwa ne matuka da aka gano kaso 22 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar ba su karbar rigakafin cututtuka da ake yi wa yara.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

“Mafi rinjaye na yaran da suka kamu da cutar, musamman wadanda suka mutu ba su taba karbar rigakafin kariya ko sau daya ba.”

Cristian, ta kara da cewa domin yaki da cutar, UNICEF ta na hadin guiwa da cibiyar binciken cututtuka ta Nijeriya (NCDC), jihohin da lamarin ya shafa, hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko ta kasa (NPHCDA), domin samar da tallafin kwararru da yadda za a dakile cutar.

Tallafin na UNICEF ya kunshi kudade, saukaka jigila wajen kai rigakafi, tuntubar masu ruwa da tsaki, kayan aiki da taimakawa a bangaren rigakafin a jihohin da lamarin ya shafa.

A cewarta sauran sun hada horas da ma’aiktan kiwon lafiya, masu bada gudunmawa, samar da takunkumin fuska, man tsaftace hannu da sauran kayan aiki.

UNICEF, ta shawarci iyaye da suke tabbatar da ‘ya’yansu suna amsar rigakafin cututtuka domin kare su daga cututtuka.

Ta kuma bukaci gwamnatoci da su tashi tsaye wajen kawo karshen cutar, inda ta ba da tabbacin ba su cikakken goyon baya domin kare yaran Nijeriya daga cutar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CutaDiphtheriaMutuwaUNICEFYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Gombe Na Bai Wa Fannin Noman Auduga  Mahimmanci – Kwamishina

Next Post

Firaministan Georgia: Bikin Bude Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Duniya Ta Chengdu Na Da Kayatarwa

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

1 hour ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 hour ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

3 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

3 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

5 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

6 hours ago
Next Post
Firaministan Georgia: Bikin Bude Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Duniya Ta Chengdu Na Da Kayatarwa

Firaministan Georgia: Bikin Bude Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Duniya Ta Chengdu Na Da Kayatarwa

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.