• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 122 A Nijeriya -UNICEF

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Diphtheria

Asusun Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), ya ce zuwa yanzu cutar mashako ta kashe rayukan yara kanana 122 a Nijeriya. 

A wata sanarwa da wakiliyar UNICEF a Nijeriya, Dokta Cristian Munduate, ta fitar a ranar Juma’a, ta ce cutar ta shafi jihohi 27 a Nijeriya.

  • Majalisa Ta Ki Amincewa Da Shirin Tinubu Na Daukar Matakin Soji A Kan Nijar
  • Manchester United Ta Dauki Hujland Daga Atalanta

Kana ta ce, zuwa watan Yulin 2023, an samu wadanda suka kamu da cutar 3,850 yayin da aka tabbatar da mutum 1,387 sun kamu da cutar.

Sanarwar, ta ce cutar ta shafi jihohin Kano, Yobe, Katsina, Lagos, Birnin tarayya Abuja, Sakkwato da Zamfara, wanda cutar ta kama a tsakanin yara ‘yan shekara 2 zuwa 14.

A cewarta, abin damuwa ne matuka da aka gano kaso 22 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar ba su karbar rigakafin cututtuka da ake yi wa yara.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

“Mafi rinjaye na yaran da suka kamu da cutar, musamman wadanda suka mutu ba su taba karbar rigakafin kariya ko sau daya ba.”

Cristian, ta kara da cewa domin yaki da cutar, UNICEF ta na hadin guiwa da cibiyar binciken cututtuka ta Nijeriya (NCDC), jihohin da lamarin ya shafa, hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko ta kasa (NPHCDA), domin samar da tallafin kwararru da yadda za a dakile cutar.

Tallafin na UNICEF ya kunshi kudade, saukaka jigila wajen kai rigakafi, tuntubar masu ruwa da tsaki, kayan aiki da taimakawa a bangaren rigakafin a jihohin da lamarin ya shafa.

A cewarta sauran sun hada horas da ma’aiktan kiwon lafiya, masu bada gudunmawa, samar da takunkumin fuska, man tsaftace hannu da sauran kayan aiki.

UNICEF, ta shawarci iyaye da suke tabbatar da ‘ya’yansu suna amsar rigakafin cututtuka domin kare su daga cututtuka.

Ta kuma bukaci gwamnatoci da su tashi tsaye wajen kawo karshen cutar, inda ta ba da tabbacin ba su cikakken goyon baya domin kare yaran Nijeriya daga cutar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Next Post
Firaministan Georgia: Bikin Bude Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Duniya Ta Chengdu Na Da Kayatarwa

Firaministan Georgia: Bikin Bude Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Duniya Ta Chengdu Na Da Kayatarwa

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.