• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ‘Yan Ta’adda Sun Sako Karin Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Da Dumi-Dumi: ‘Yan Ta’adda Sun Sako Karin Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan tattaunawa sosai tare da shiga tsakani ta kai ga sako karin fasinjoji 11 na jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna da aka yi garkuwa da su a ranar 28 ga Maris, 2022.

Hadimin Sheikh Dakta Ahmad Abubakar Gumi, Malam Tukur Mamu (Dan-Iyan) Fika) ne ya shiga tsakani har aka ga sake sakin wasu bakwai daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a ranar Asabar.

  • NSCDC Ta Bankado Shirin ISWAP Na Kai Hare-Hare A Makarantu Da Cocina A Abuja
  • ‘Yan Nijeriya Sun Yi Alhinin Rasuwar Babban Sakataren OPEC Sanusi Barkindo

Wadanda aka saki a ranar Asabar sun hada da Bosede Olurotimi, Abubakar Zubairu, Alhassan Sule da Sadiq Ango Abdullahi.

Sauran fasinjojin da suka yi sa’a sun hada da Muhammad Daiyabu Paki, Aliyu Usman da kuma wani dan kasar waje daya tilo dan asalin kasar Pakistan, Dr. Muhammad Abuzar Afzal.

Da yake magana kan lamarin, Mamu ya ce nasarar da aka samu a ranar Asabar din na sakin wadanda lamarin ya rutsa da su ya tabbatar da muhimmancin sulhu da Sheikh Dr. Ahmad Gumi ke yi a tsakanin ‘yan bindiga.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

“Ina so in tabbatar wa al’umma cewa, duk abin da ya faru a yau, ni kadai ne ya kaddamar da shi tare da cikakken goyon baya da addu’a daga shugabana, Sheikh Gumi.

“Don haka ina jaddada cewa gwamnati na da ikon ceto wadanda ba su ji ba ba su gani ba a rana daya. Wannan mutum daya ne kawai da ya sadaukar da rayuwarsa. Babu wata hanyar soja da za ta magance tabarbarewar tsaro a Nijeriya.

“A duk abin da nake yi, ba na bukata ko kuma bukatar wani lada a wurin kowa sai dai daga wurin Allah kuma ina fatan al’ummar da muka sadaukar da rayuwarmu za su fahimci hakan,” in ji Mamu.

Mai sasantawar ya kara da cewa an mika wadanda aka sako su bakwai ga sojoji kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta zuwa Kaduna.

“Wurin da su (masu garkuwa) suka bayar yana da nisa da kuma hadari. Akwai shingen binciken sojoji kafin kutsawa cikin dajin,” ya bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAngo AbdullahiAsabarFasinjojin Jirgin Kasan Abuja-KadunaHariKubuta
ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Bankado Shirin ISWAP Na Kai Hare-Hare A Makarantu Da Cocina A Abuja

Next Post

Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Yin Hadin Gwiwa Game Da Samar Da Isasshen Abinci A Duniya A Taron G20

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

15 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

24 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Yin Hadin Gwiwa Game Da Samar Da Isasshen Abinci A Duniya A Taron G20

Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Yin Hadin Gwiwa Game Da Samar Da Isasshen Abinci A Duniya A Taron G20

LABARAI MASU NASABA

Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.