ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ‘Yan Ta’adda Sun Sako Karin Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna

by Sadiq
4 years ago
Fasinjoji

Bayan tattaunawa sosai tare da shiga tsakani ta kai ga sako karin fasinjoji 11 na jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna da aka yi garkuwa da su a ranar 28 ga Maris, 2022.

Hadimin Sheikh Dakta Ahmad Abubakar Gumi, Malam Tukur Mamu (Dan-Iyan) Fika) ne ya shiga tsakani har aka ga sake sakin wasu bakwai daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a ranar Asabar.

  • NSCDC Ta Bankado Shirin ISWAP Na Kai Hare-Hare A Makarantu Da Cocina A Abuja
  • ‘Yan Nijeriya Sun Yi Alhinin Rasuwar Babban Sakataren OPEC Sanusi Barkindo

Wadanda aka saki a ranar Asabar sun hada da Bosede Olurotimi, Abubakar Zubairu, Alhassan Sule da Sadiq Ango Abdullahi.

ADVERTISEMENT

Sauran fasinjojin da suka yi sa’a sun hada da Muhammad Daiyabu Paki, Aliyu Usman da kuma wani dan kasar waje daya tilo dan asalin kasar Pakistan, Dr. Muhammad Abuzar Afzal.

Da yake magana kan lamarin, Mamu ya ce nasarar da aka samu a ranar Asabar din na sakin wadanda lamarin ya rutsa da su ya tabbatar da muhimmancin sulhu da Sheikh Dr. Ahmad Gumi ke yi a tsakanin ‘yan bindiga.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Ina so in tabbatar wa al’umma cewa, duk abin da ya faru a yau, ni kadai ne ya kaddamar da shi tare da cikakken goyon baya da addu’a daga shugabana, Sheikh Gumi.

“Don haka ina jaddada cewa gwamnati na da ikon ceto wadanda ba su ji ba ba su gani ba a rana daya. Wannan mutum daya ne kawai da ya sadaukar da rayuwarsa. Babu wata hanyar soja da za ta magance tabarbarewar tsaro a Nijeriya.

“A duk abin da nake yi, ba na bukata ko kuma bukatar wani lada a wurin kowa sai dai daga wurin Allah kuma ina fatan al’ummar da muka sadaukar da rayuwarmu za su fahimci hakan,” in ji Mamu.

Mai sasantawar ya kara da cewa an mika wadanda aka sako su bakwai ga sojoji kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta zuwa Kaduna.

“Wurin da su (masu garkuwa) suka bayar yana da nisa da kuma hadari. Akwai shingen binciken sojoji kafin kutsawa cikin dajin,” ya bayyana.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Yin Hadin Gwiwa Game Da Samar Da Isasshen Abinci A Duniya A Taron G20

Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Yin Hadin Gwiwa Game Da Samar Da Isasshen Abinci A Duniya A Taron G20

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.