• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ‘Yan Ta’adda Sun Sako Karin Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Da Dumi-Dumi: ‘Yan Ta’adda Sun Sako Karin Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan tattaunawa sosai tare da shiga tsakani ta kai ga sako karin fasinjoji 11 na jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna da aka yi garkuwa da su a ranar 28 ga Maris, 2022.

Hadimin Sheikh Dakta Ahmad Abubakar Gumi, Malam Tukur Mamu (Dan-Iyan) Fika) ne ya shiga tsakani har aka ga sake sakin wasu bakwai daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a ranar Asabar.

  • NSCDC Ta Bankado Shirin ISWAP Na Kai Hare-Hare A Makarantu Da Cocina A Abuja
  • ‘Yan Nijeriya Sun Yi Alhinin Rasuwar Babban Sakataren OPEC Sanusi Barkindo

Wadanda aka saki a ranar Asabar sun hada da Bosede Olurotimi, Abubakar Zubairu, Alhassan Sule da Sadiq Ango Abdullahi.

Sauran fasinjojin da suka yi sa’a sun hada da Muhammad Daiyabu Paki, Aliyu Usman da kuma wani dan kasar waje daya tilo dan asalin kasar Pakistan, Dr. Muhammad Abuzar Afzal.

Da yake magana kan lamarin, Mamu ya ce nasarar da aka samu a ranar Asabar din na sakin wadanda lamarin ya rutsa da su ya tabbatar da muhimmancin sulhu da Sheikh Dr. Ahmad Gumi ke yi a tsakanin ‘yan bindiga.

Labarai Masu Nasaba

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

“Ina so in tabbatar wa al’umma cewa, duk abin da ya faru a yau, ni kadai ne ya kaddamar da shi tare da cikakken goyon baya da addu’a daga shugabana, Sheikh Gumi.

“Don haka ina jaddada cewa gwamnati na da ikon ceto wadanda ba su ji ba ba su gani ba a rana daya. Wannan mutum daya ne kawai da ya sadaukar da rayuwarsa. Babu wata hanyar soja da za ta magance tabarbarewar tsaro a Nijeriya.

“A duk abin da nake yi, ba na bukata ko kuma bukatar wani lada a wurin kowa sai dai daga wurin Allah kuma ina fatan al’ummar da muka sadaukar da rayuwarmu za su fahimci hakan,” in ji Mamu.

Mai sasantawar ya kara da cewa an mika wadanda aka sako su bakwai ga sojoji kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta zuwa Kaduna.

“Wurin da su (masu garkuwa) suka bayar yana da nisa da kuma hadari. Akwai shingen binciken sojoji kafin kutsawa cikin dajin,” ya bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAngo AbdullahiAsabarFasinjojin Jirgin Kasan Abuja-KadunaHariKubuta
ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Bankado Shirin ISWAP Na Kai Hare-Hare A Makarantu Da Cocina A Abuja

Next Post

Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Yin Hadin Gwiwa Game Da Samar Da Isasshen Abinci A Duniya A Taron G20

Related

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

9 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

14 hours ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

17 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

20 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

21 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

1 day ago
Next Post
Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Yin Hadin Gwiwa Game Da Samar Da Isasshen Abinci A Duniya A Taron G20

Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Yin Hadin Gwiwa Game Da Samar Da Isasshen Abinci A Duniya A Taron G20

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.