• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sahara

Jama’a, ko kun taba ganin furannin Rose da suka bude a cikin hamada? 

Lallai, wannan abu ne da ya faru a hakika a hamadar Taklimakan da ke kasar Sin. A kwanan nan, furannin Rose kimanin dubu 100 ne suka bude a iyakar hamadar, lamarin da ya shaida karin nasara da kasar Sin ta samu ta fannin yaki da kwararar hamada.

Taklimakan tana jihar Xinjiang da ke arewa maso yammacin kasar Sin, hamada ce mafi girma ta kasar Sin, wadda kuma ta kasance muhimmin fagen yaki da kwararar hamada a kasar Sin. A sassan kudancin hamadar da aka fi samun iska mai karfi, tuddan rairayi su kan mamaye dausayi da kimanin mita 2 zuwa 5 a kowace shekara, kuma yadda za a tsayar da hamadar babban aiki ne da jihar ta Xinjiang ke sanyawa gaba wajen kiyaye muhalli. Bisa kokarin da masanan yaki da kwararar hamada da ma mazauna wurin suka shafe gomman shekaru suna yi, daga karshe suka cimma nasarar kewaye hamadar da wani shingen itatuwa mai tsawon kilomita 3046 a ranar 28 ga watan Nuwamban bara, shingen da ya kasance irinsa mafi tsawo da aka kafa a duniya. Furannin Rose da suka bude kwanan nan kuma, sun kasance sashe na karshe da aka dasa a wannan babban aiki. Bisa nazarin da masu binciken kimiyya na wurin suka yi a kan hamada da bugowar iska da ma yanayin ruwa na wurin, sun gano dabarar dasa furannin Rose da suka iya jure yanayin hamadar, har ma ga shi a yau, furannin sun zamanto wani shinge mai karfi da ke iya kare iska da ma rairayi.

A hakika, shingen itatuwa da aka yi amfani da shi wajen kewaya hamadar Taklimakan wani misali ne da ya shaida gaggaruman nasarorin da kasar Sin ta samu ta fannin yaki da kwararar hamada. Daga hamadar Maowusu zuwa Kubuqi, cikin gomman shekaru da suka wuce, kasar Sin ta samu nasarorin a-zo-a-gani ta fannin yaki da kwararar hamada, har ma ta samu babban yabo daga gamayyar kasa da kasa.

Ba a kasar Sin kadai ba ce, kwararar hamada kalubale ne ga kasashen duniya baki daya. A nahiyar Afirka, matsalar ta dade tana addabar kasashen yankin Sahel. A kasar Mauritania, kusan kashi 2/3 na fadin kasar na cikin hamadar Sahara, kuma matsalolin fari na kwararar hamada suna haifar da munanan illoli ga ci gaban kasar. Sai dai yanayin ya fara sauyawa. A kauyen Bir El Barka na yankin Trarza da ke yammacin kasar, an shimfida bututun ban ruwa nau’in ‘drip irrigation’ a Turance, ga shi kuma tsiron ganyayen lambu sun fito daga gonar rairayi. A gefen gonar kuma, allunan samar da wutar lantarki ta hasken rana suna samar da lantarki ga famfuna don fitar da ruwa daga karkashin kasa zuwa gonaki. Lallai wannan lambun nune-nunen fasahohin yaki da kwararar hamada na tsakanin Sin da kasashen Afirka reshen kasar Mauritania ya kayatar sosai. A can wajen, bisa gudummawar da masanan kasar Sin suka bayar, an mai da hamadar ta zama dausayi bisa ingantattun fasahohi na kasar Sin, har ma an kai ga yin gwajin shuka nau’o’in amfanin gona tare da samun girbin wasunsu.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Sinawa tun zamanin baya na ganin cewa, samun dadi ga kowa shi ne dadi na gaske. A zamanin yanzu, kasar Sin ba kawai take jin dadin sauye-sauyen da ke faruwa a sassan hamada na kasar ba, hatta ma tana fatan ganin karin yankunan hamada sun zama dausayi a fadin duniya. Don haka, take kokarin bayar da fasahohinta ga kasashen Afirka da su ma suke fuskantar kalubalen kwararar hamada. Bisa nazarin da masanan Sin da kasashen Afirka suka yi, sun gano cewa, fadin sassan hamada a yankin Sahel ya ragu daga kaso 72,31% zuwa 69.23% tsakanin shekarar 2000 zuwa ta 2020.

Daga Taklimakan zuwa Sahara, karin abubuwan al’ajabi na ci gaba da faruwa bisa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ta fannin yaki da kwararar hamada.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Next Post
Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.