• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 hours ago
in Ra'ayi Riga
0
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jama’a, ko kun taba ganin furannin Rose da suka bude a cikin hamada? 

Lallai, wannan abu ne da ya faru a hakika a hamadar Taklimakan da ke kasar Sin. A kwanan nan, furannin Rose kimanin dubu 100 ne suka bude a iyakar hamadar, lamarin da ya shaida karin nasara da kasar Sin ta samu ta fannin yaki da kwararar hamada.

Taklimakan tana jihar Xinjiang da ke arewa maso yammacin kasar Sin, hamada ce mafi girma ta kasar Sin, wadda kuma ta kasance muhimmin fagen yaki da kwararar hamada a kasar Sin. A sassan kudancin hamadar da aka fi samun iska mai karfi, tuddan rairayi su kan mamaye dausayi da kimanin mita 2 zuwa 5 a kowace shekara, kuma yadda za a tsayar da hamadar babban aiki ne da jihar ta Xinjiang ke sanyawa gaba wajen kiyaye muhalli. Bisa kokarin da masanan yaki da kwararar hamada da ma mazauna wurin suka shafe gomman shekaru suna yi, daga karshe suka cimma nasarar kewaye hamadar da wani shingen itatuwa mai tsawon kilomita 3046 a ranar 28 ga watan Nuwamban bara, shingen da ya kasance irinsa mafi tsawo da aka kafa a duniya. Furannin Rose da suka bude kwanan nan kuma, sun kasance sashe na karshe da aka dasa a wannan babban aiki. Bisa nazarin da masu binciken kimiyya na wurin suka yi a kan hamada da bugowar iska da ma yanayin ruwa na wurin, sun gano dabarar dasa furannin Rose da suka iya jure yanayin hamadar, har ma ga shi a yau, furannin sun zamanto wani shinge mai karfi da ke iya kare iska da ma rairayi.

A hakika, shingen itatuwa da aka yi amfani da shi wajen kewaya hamadar Taklimakan wani misali ne da ya shaida gaggaruman nasarorin da kasar Sin ta samu ta fannin yaki da kwararar hamada. Daga hamadar Maowusu zuwa Kubuqi, cikin gomman shekaru da suka wuce, kasar Sin ta samu nasarorin a-zo-a-gani ta fannin yaki da kwararar hamada, har ma ta samu babban yabo daga gamayyar kasa da kasa.

Ba a kasar Sin kadai ba ce, kwararar hamada kalubale ne ga kasashen duniya baki daya. A nahiyar Afirka, matsalar ta dade tana addabar kasashen yankin Sahel. A kasar Mauritania, kusan kashi 2/3 na fadin kasar na cikin hamadar Sahara, kuma matsalolin fari na kwararar hamada suna haifar da munanan illoli ga ci gaban kasar. Sai dai yanayin ya fara sauyawa. A kauyen Bir El Barka na yankin Trarza da ke yammacin kasar, an shimfida bututun ban ruwa nau’in ‘drip irrigation’ a Turance, ga shi kuma tsiron ganyayen lambu sun fito daga gonar rairayi. A gefen gonar kuma, allunan samar da wutar lantarki ta hasken rana suna samar da lantarki ga famfuna don fitar da ruwa daga karkashin kasa zuwa gonaki. Lallai wannan lambun nune-nunen fasahohin yaki da kwararar hamada na tsakanin Sin da kasashen Afirka reshen kasar Mauritania ya kayatar sosai. A can wajen, bisa gudummawar da masanan kasar Sin suka bayar, an mai da hamadar ta zama dausayi bisa ingantattun fasahohi na kasar Sin, har ma an kai ga yin gwajin shuka nau’o’in amfanin gona tare da samun girbin wasunsu.

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

Sinawa tun zamanin baya na ganin cewa, samun dadi ga kowa shi ne dadi na gaske. A zamanin yanzu, kasar Sin ba kawai take jin dadin sauye-sauyen da ke faruwa a sassan hamada na kasar ba, hatta ma tana fatan ganin karin yankunan hamada sun zama dausayi a fadin duniya. Don haka, take kokarin bayar da fasahohinta ga kasashen Afirka da su ma suke fuskantar kalubalen kwararar hamada. Bisa nazarin da masanan Sin da kasashen Afirka suka yi, sun gano cewa, fadin sassan hamada a yankin Sahel ya ragu daga kaso 72,31% zuwa 69.23% tsakanin shekarar 2000 zuwa ta 2020.

Daga Taklimakan zuwa Sahara, karin abubuwan al’ajabi na ci gaba da faruwa bisa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ta fannin yaki da kwararar hamada.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

Next Post

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

Related

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

3 days ago
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Ra'ayi Riga

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

6 days ago
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

1 week ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 week ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

2 weeks ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

June 17, 2025
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

June 17, 2025
Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

June 17, 2025
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

June 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

June 17, 2025
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

June 17, 2025
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.