• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta kara fadawa cikin wani sabon rikici bayan kwanciyar hankali da aka samu, a daidai lokacin da jam’iyyar take shirin gudanar da babban taronta na kasa a ranar 15 ga Nuwamba.

PDP ta kara fadawa rikicin cikin gida ne a daidai lokacin da shugaban jam’iyyar na kasa, Ambasada Umar Damagum da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, suka samu rashin jituwa kan yadda aka gudanar da zabe a jihohi uku da suka hada da Kuros Ribas da Kebbi da Filato.

  • Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

An dai shirya za a gudanar da zaben shugabannin PDP na jihohi a ranar Asabar, 27 ga Satumba. Sai dai kuma kasa da awanni 48 kafin fara babban taron, kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar karkashin jagorancin Damagum ya rubuta wa hukumar zabe ta kasa (INEC) sanarwar dage zaben, bisa abin da suka kira lamuran da ba a za ta ba.

A wani bangare na wasikar da Damagum ya aika wa INEC ya ce, “Kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyarmu yana dakatar da babban taron jihohi a Korus Ribas da Filato da Kebbi. Za a sanar wa hukumar zabe sabon ranar da za a gudanar da taron.”

A wani mataki da ke nuna rashin jituwa a cikin kwamitin gudanarwar, Sanata Anyanwu ya rubuta wasika ta mayarwa ga INEC, yana ba da shawarar ga shugaban INEC da ya yi watsi da dage zaben da shugaban jam’iyyar ya bukata.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Anyanwu a cikin wasikarsa ya bayyana cewa an kammala dukkan shirye-shirye wasu tsare-tsare don gudanar da taron, kuma za a gudana da shi kamar yadda aka tsara.

“Muna tabbatar wa hukumar zabe cewa za mu gudanar da taron kamar yadda aka tsara tun farko ba tare da dagawa ba.

“Ya kamata hukumar zabe ta yi watsi da wasikar da shugaban jam’iyyar ya tura mata tun da farko na dage toron,” ya aika wa INEC wasikar ne a ranar 26 ga Satumba ba tare da sa hannunna ba.

A cewar sakataren, bai kamata INEC ta yi aiki kan wata wasikar da ba sanya hannunsa hade da na Damagum ba.

Wata majiyar ta bayyana cewa abin da ke faruwa yanzu ya nuna yadda kowani bangare ke kokarin mallakan iko a jam’iyyar PDP.

A ranar Alhamis da ta gabata, sakataren yada labarai na jam’iyyar, Debo Ologunagba, ya bayyana matakin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na dage tarukan jam’iyyar, musamman na jihohin Filato da Kuros Ribas zuwa sabbin ranaku, wadanda za a sanar da su a nan gaba kadan.

“Kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya bukaci dukkan shugabanni da masu ruwa da tsaki da daukacin mambobin PDP da hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) da kafofin watsa labarai da hukumomin tsaro da jama’a gaba daya tana sanar da su dage lokacin zabe kuma su bi ka’idojinta da suka dace,” in ji Ologunagba.

Bincike ya nuna cewa kwamitin zabe na PDP da aka kafa don gudanar da taron a Jihar Kuros Ribas sun gudanar da zaben a ranar Asabar.

Kwamitin, wanda Honourable Jones Chukwudi Onyereri ya shugabanta, ya yi watsi da umarnin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na dage zaben.

Jam’iyyar ta yi zazzafar muhawara kan wannan lamari, wanda hakan ya kara ruruta wutar rikicin cikin gida na jam’iyyar PDP.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.