• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Tarihi
0
Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mulkin mallaka wata hanya ce ta tafiyar da gwamnati inda Turawan Ingila suka yi amfani da Sarakunan gargajiya wajen tafiyar da harkokin mulkinsu a yammacin Afirka. Shugaban ko jagoran al’amarin mulkin mallaka a yammacin Afirka shi ne Lord Frederick Lugard a shekarar1906.Ya fara gwada tafiyar da tsarin mulkin ne a Arewacin Nijeriya lokacin da aka ga abin an samu nasara,sai aka fara amfani da shi a sauran sassan kasashen yammacin Afirka.

An amince da Sarakunan gargajiya
Sarakuna wadanda sune ke lura da al’amuran da suka shafi al’umma a Arewacin Nijeriya al’umma suka nada su,don haka aka amince da sub a tare da wata matsala ba.Sune suka jagoranci hukumomin da ake tafiyar da al’amuran da suka shafi al’umma da ake kiran su da suna Natibe Authority. Shi ya sa babu wata matsala idan Sarakuna suka bayar da umarnin daya zo daga wurin jami’an Turawa na yin wani abu,hakan ta kasance ne saboda al’umma sun saba da samun umarni na wani abu daga wurin Sarakunan.

Sarakunan gargajiya ba su wasa da ba da umarni
Lokacin da gwamna Lord Lugard ya aiwatar da mulkin mallaka na Turawan Ingila a Arewacin Nijeriya,tun kafin lokacin da akwai hanyar da ake tafiyar da sarautar gargajiya ta tafiyar da al’umma.Sarakunan ko Sultan tuni akwai wuraren da suke karkashinsu suna mulkarsu ba tare da matsala ba,mutane kuma sun saba da al’amarin. Shi yasa mulkin ba a samu wata matsalar tafiyar da shi ba wanda yake da alaka da siyasa.

Al’amarin Haraji
Al’ummar Arewacin Nijeriya sun saba da al’amarin daya shafi Haraji saboda kuwa Talakawa sun saba da biyan Haraji nau’oi daban daban da suka hada da Jangali na dabbobi da wadanda mutane suke biya,shi yasa ba a samu wata matsala ba domin al’ummar Arewa sun saba da biyan su nau’oin harajin,domin an samu yin gyara ne lokacin da aka bullo da shi lokacin da aka fara tafiyar da mulkin mallaka a Arewacin Nijeriya.

Rashin Masu Ilmin Zamani A Arewa
A Arewacin Nijeriya bamasu ilimin zamani a lokacin kamar yadda ake da su a Kudancin Nijeriya,saboda a lokacin a Arewacin Nijeriya akwai lauyoyi wadanda suka samu horo a Ingila da kuma ‘yan jarida,alal misali a Arewacin Nijeriya ba irin wadancan mutanen wadanda Turawan mulkin mallaka za su samu matsalar tunkararsu,ba kamar a Kudancin Nijeriya ba.

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Kotunan shariar musulunci
Mulkin mallaka na turawan Ingila ya samu nasara ne a Arewacin Nijeriya saboda dam tuni ana da tsarin shari’a karamar hukumar gargajiya da ake kira Natibe Authority a lokacin.Sarakuna a Arewacin Nijeriya suna da kotu inda ake shari’ar wadanda suka aikata laifi idan kuma aka samu mutum da aikata laifi ana iya yanke ma shi hukunci, wannan tsarin ne Lord Lugard ya amince da shi da yi ma shi gyara.Misali kotunan musulunci ba za su zartar da hukunci kisa ba, ba tare da amincewar jami’an Turawan mulkin mallaka da suke zaune a Larduna daban- daban a Nijeriya.

Umarnin Jami’an Ingila
Kasancewar jami’an Turawan Ingila a Arewacin Nijeriya inda suke kulawa da Larduna ana kiransu da sunan Rasdan sune suke ba Sarakunan gargajiya shawarwari, wanda hakan ne ya basu dama ta samun nasara a tafiyar da mulkinsu a Arewacin Nijeriya.Kwamishinonin Larduna su suka rika ba Sarakunan gargajiya a Arewa shawarar da ta tabbatar da mulkin Turawan Ingila ya samu nasara a yammacin Afirka.daudawa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaBirtaniyaMulkin Mallaka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Ya Faru Tsakanin Ukraine Da Rasha Bayan Barkewar Yaki A Gaza

Next Post

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

Related

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

1 month ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

1 month ago
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
Tarihi

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

2 months ago
Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

5 months ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

5 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

10 months ago
Next Post
Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.