ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Gwamnan Gombe Ya Kaddamar Da Sayar Da Taki Mai Rahusa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Gwamnan Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya kaddamar da sayar da takin zamani na daminar bana da nufin bunkasa noma a jihar.

Da yake kaddamar da takin a gidan gona na Lawanti da ke karamar hukumar Akko, gwamnan ya ce za a sayar da takin ne kan kudi Naira 19,000 kan kowane buhu, sabanin farashin kasuwa da ya kai kusan Naira 26,000, don samarwa manoman jihar sauki.

  • EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa’o’i
  • Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

Gwamnan ya ce, “Gwamnati ta sayo tirela 160 na takin kan kudi Naira biliyan biyu da miliyan dari takwas da talatin, karin kimanin tireloli 35 kenan a kan na bara.”

ADVERTISEMENT

Don tabbatar da cewa takin ya kai ga ainihin manoma, Gwamna Inuwa ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samar da ingantaccen tsarin sayar da shi a dukkan gundumomin jihar 114 don tabbatar da cewa takin ya kai ga manoma na hakika tun daga tushe.

“Mun fahimci cewa tsadar taki da sauran kayayyakin amfanin gona na iya zama babban cikas ga manomanmu, don haka ne muke aiki tukuru wajen samar da wannan taki a farashi mai rahusa don ragewa manomanmu dawainiyar kudi.

LABARAI MASU NASABA

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

“Burinmu shi ne mu tallafa musu da muhimman kayan aikin noma don bunkasa amfanin gona da inganta kasa, da habaka ribar da suke samu, da kuma tabbatar da dorewar harkokin noma a jiharmu”.

Gwamnan ya ce gwamnatinsa ta gudanar da ayyuka da shirye-shirye daban-daban na inganta harkar noma a Gombe, don haka jihar ta shiga cikin harkoki da tsare-tsaren noma da dama a matakin jiha da shiyya da kuma kasa baki daya don bunkasa harkar ta noma.

“Gwamnati ta kuma samar da shirin tallafi na ‘NG-cares’ don samar da taki da sinadaran noma ga manomanmu kyauta, mun kuma hada gwiwa da ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya wajen horar da manoma kan noman masara da doya, inda aka bai wa wadanda suka amfana kayan aikin da suka dace don nomansu.”

Sai ya yi kira ga manoman su bai wa wadanda aka dorawa alhakin sayar da takin da rarraba shi a fadin jihar hadin kai don samun nasarar aikin.

Ya kuma gargade su, da su guji karkatar da takin.

Ya kara da cewa Jihar Gombe jiha ce ta noma, inda fiye da kaso 80 cikin dari na al’ummarta manoma ne, “Saboda haka tallafawa wannan bangare yana da matukar muhimmanci ga ci gaban tattalin arziki, da samar da abinci, da dorewar rayuwar jama’armu”.

Tun farko a jawabinsa na maraba, Daraktan Tsare-Tsare, Bincike da Kididdiga a Ma’aikatar Noma da Kiwo, Dakta Ibrahim Yakubu Usman, ya ce, an kafa kwamitocin yaki da rikicin makiyaya da manoma don magance rikice-rikice da allurar rigakafin cututtukan dabbobi masu yaduwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
Labarai

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola
Manyan Labarai

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Next Post
Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

LABARAI MASU NASABA

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.