• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Gwamnan Gombe Ya Kaddamar Da Sayar Da Taki Mai Rahusa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Daminar Bana: Gwamnan Gombe Ya Kaddamar Da Sayar Da Taki Mai Rahusa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya kaddamar da sayar da takin zamani na daminar bana da nufin bunkasa noma a jihar.

Da yake kaddamar da takin a gidan gona na Lawanti da ke karamar hukumar Akko, gwamnan ya ce za a sayar da takin ne kan kudi Naira 19,000 kan kowane buhu, sabanin farashin kasuwa da ya kai kusan Naira 26,000, don samarwa manoman jihar sauki.

  • EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa’o’i
  • Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

Gwamnan ya ce, “Gwamnati ta sayo tirela 160 na takin kan kudi Naira biliyan biyu da miliyan dari takwas da talatin, karin kimanin tireloli 35 kenan a kan na bara.”

Don tabbatar da cewa takin ya kai ga ainihin manoma, Gwamna Inuwa ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samar da ingantaccen tsarin sayar da shi a dukkan gundumomin jihar 114 don tabbatar da cewa takin ya kai ga manoma na hakika tun daga tushe.

“Mun fahimci cewa tsadar taki da sauran kayayyakin amfanin gona na iya zama babban cikas ga manomanmu, don haka ne muke aiki tukuru wajen samar da wannan taki a farashi mai rahusa don ragewa manomanmu dawainiyar kudi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

“Burinmu shi ne mu tallafa musu da muhimman kayan aikin noma don bunkasa amfanin gona da inganta kasa, da habaka ribar da suke samu, da kuma tabbatar da dorewar harkokin noma a jiharmu”.

Gwamnan ya ce gwamnatinsa ta gudanar da ayyuka da shirye-shirye daban-daban na inganta harkar noma a Gombe, don haka jihar ta shiga cikin harkoki da tsare-tsaren noma da dama a matakin jiha da shiyya da kuma kasa baki daya don bunkasa harkar ta noma.

“Gwamnati ta kuma samar da shirin tallafi na ‘NG-cares’ don samar da taki da sinadaran noma ga manomanmu kyauta, mun kuma hada gwiwa da ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya wajen horar da manoma kan noman masara da doya, inda aka bai wa wadanda suka amfana kayan aikin da suka dace don nomansu.”

Sai ya yi kira ga manoman su bai wa wadanda aka dorawa alhakin sayar da takin da rarraba shi a fadin jihar hadin kai don samun nasarar aikin.

Ya kuma gargade su, da su guji karkatar da takin.

Ya kara da cewa Jihar Gombe jiha ce ta noma, inda fiye da kaso 80 cikin dari na al’ummarta manoma ne, “Saboda haka tallafawa wannan bangare yana da matukar muhimmanci ga ci gaban tattalin arziki, da samar da abinci, da dorewar rayuwar jama’armu”.

Tun farko a jawabinsa na maraba, Daraktan Tsare-Tsare, Bincike da Kididdiga a Ma’aikatar Noma da Kiwo, Dakta Ibrahim Yakubu Usman, ya ce, an kafa kwamitocin yaki da rikicin makiyaya da manoma don magance rikice-rikice da allurar rigakafin cututtukan dabbobi masu yaduwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DaminaGombeInuwa MuhammadTakiTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa’o’i

Next Post

Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

48 minutes ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

4 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

6 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

8 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

9 hours ago
Next Post
Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

LABARAI MASU NASABA

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.