• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Sun Dukufa Wajen Warware Rikicin Siyasar Da Ta Kunno Kai A Kungiyar ACF

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
Arewa

Wasu jiga-jigan masu fada a ji a yankin arewa sun shiga tsakani don warware rikicin siyasar da kunno kai bayan dakatarwar da shugaban kwamitin zartarwa na kungiyar Arewa ‘Consultatibe Forum’ (ACF), Mista Mamman Mike Osuman.

Mataimakin Shugaban Kwamitin Amintattu (BoT), Ambasada Ibrahim Maisule ne ya tabbatar da hakan a wata tattaunawa ta musamman a Abuja.

  •  Ali Nuhu Ya Zama Jakadan Kamfanin Tsaftace Haƙora A Arewacin Nijeriya 
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

A karshen makon da ya gabata ne dai aka dakatar da shugaban kwamitin zartarwa na kungiyar ACF bisa wasu kalamai da ya yi da suka shafi siyasa, wadanda kwamitin amintattu da wasu mambobin kungiyar suka yi watsi da su.

A cikin wata wasika tare da sa hannun babban sakataren kungiyar ACF, Malam Murtala Aliyu da shugabannin BoT, Alhaji Bashir Dalhatu, Mista Osuman, an zargi Mista Osuman da yin kalamai marasa izini da ke nuna cewa arewa za ta mara wa dan takarar shugaban kasa daga arewa baya a 2027.

Wasikar ta ci gaba da cewa, “An jawo hankalin kungiyar kan wasu bayanai da aka rika yadawa ga Mista Mamman Mike Osuman, SAN, OFR, Shugaban kwamitin zartarwa na ACF na kasa, wadanda aka yi a yayin taron kungiyar wanda aka yi a ranar Laraba, 20 ga Nuwamba, 2024, a hedkwatar ACF da ke Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

“An ji Mista Osuman yana cewa arewa za ta mara wa dan takarar shugaban kasa daga arewa baya a 2027. Shugaban kungiyar ya yi wadannan kalamai ne ba tare da tuntuba ko tattaunawa da wasu shugabanni da mambobin kungiyar ta ACF ba, don haka ya nuna ra’ayinsa ne kwai.

“ACF ta yi watsi da kalaman Mista Mamman Mike Osuman gaba daya. Don haka ne shugabannin kwamitin amintattu na ACF (BOT) da na gudanarwa ta NEC suka yanke shawarar dakatar da Mista Mamman Mike Osuman nan take.”

Sai dai Mista Osuman, ya yi zargin cewa ba a yi masa adalci ba wajen tsarin da aka bi na dakatar da shi.

An dai bayyana cewa, Mista Osuman ya tara tawagar manyan lauyoyin ne tun a karshen makon da ya gabata, a shirye-shiryen shigar da karar na kalubalantar dakatar da shi daga mukaminsa.

Wasu majiyoyi na kusa da shi sun ce ya tattara manyan lauyoyin Nijeriya guda takwas masu mukamin SANs da nufin kalubalantar dakatar da shi a kotu.

Bugu da kari, wasu majiyoyi na kusa da BoT da kuma NEC na kungiyar sun shaida cewa tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Alhaji Mahmud Yayale Ahmed ya kira taron masu ruwa da tsaki a ranar Talata a Abuja, inda suka tattauna kan bukatar gaggawa don magance rikicin wajen guje jefa ACF cikin wani babban rikicin siyasa.

An tattaro cewa, za a ci gaba da taron ne a ranar Asabar, yayin da karin shugabanni a yankin arewa ke kokarin ganin an shawo kan rikicin cikin gaggawa.

Ambasada Maisule ya bayyana kwarin gwiwa game da shirin sulhun, inda ya ce dattawan yankin sun dukufa wajen ganin an warware matsalar.

“Mutane suna yin kuskure a kowani lokaci, mu mutane ne amma kuskure ba za a taba sanya shi ba a matsayin daidai. Don haka dole ne a nemo mafita.

“Tattaunawa da cikakkun bayanai a bainar jama’a yanzu bai zama dole ba, saboda an riga an yi wani babban yunkuri na warware rikicin. Wadanda ke da hannu a cikin yunkurin suna da himma sosai kuma suna iya aikin.

“Na yi imani da iyawarsu na nemo hanyar warware matsalar, kuma ina da kyakkyawan fata game da sakamakon lamarin. A wurina, babban abu mai muhimmanci shi ne, kawar zargi tare da tallafa wa tsarin don tabbatar da ci gaba. A nan ne hankalina ya karkata,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.