ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Sun Dukufa Wajen Warware Rikicin Siyasar Da Ta Kunno Kai A Kungiyar ACF

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Arewa

Wasu jiga-jigan masu fada a ji a yankin arewa sun shiga tsakani don warware rikicin siyasar da kunno kai bayan dakatarwar da shugaban kwamitin zartarwa na kungiyar Arewa ‘Consultatibe Forum’ (ACF), Mista Mamman Mike Osuman.

Mataimakin Shugaban Kwamitin Amintattu (BoT), Ambasada Ibrahim Maisule ne ya tabbatar da hakan a wata tattaunawa ta musamman a Abuja.

  •  Ali Nuhu Ya Zama Jakadan Kamfanin Tsaftace Haƙora A Arewacin Nijeriya 
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

A karshen makon da ya gabata ne dai aka dakatar da shugaban kwamitin zartarwa na kungiyar ACF bisa wasu kalamai da ya yi da suka shafi siyasa, wadanda kwamitin amintattu da wasu mambobin kungiyar suka yi watsi da su.

ADVERTISEMENT

A cikin wata wasika tare da sa hannun babban sakataren kungiyar ACF, Malam Murtala Aliyu da shugabannin BoT, Alhaji Bashir Dalhatu, Mista Osuman, an zargi Mista Osuman da yin kalamai marasa izini da ke nuna cewa arewa za ta mara wa dan takarar shugaban kasa daga arewa baya a 2027.

Wasikar ta ci gaba da cewa, “An jawo hankalin kungiyar kan wasu bayanai da aka rika yadawa ga Mista Mamman Mike Osuman, SAN, OFR, Shugaban kwamitin zartarwa na ACF na kasa, wadanda aka yi a yayin taron kungiyar wanda aka yi a ranar Laraba, 20 ga Nuwamba, 2024, a hedkwatar ACF da ke Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

“An ji Mista Osuman yana cewa arewa za ta mara wa dan takarar shugaban kasa daga arewa baya a 2027. Shugaban kungiyar ya yi wadannan kalamai ne ba tare da tuntuba ko tattaunawa da wasu shugabanni da mambobin kungiyar ta ACF ba, don haka ya nuna ra’ayinsa ne kwai.

“ACF ta yi watsi da kalaman Mista Mamman Mike Osuman gaba daya. Don haka ne shugabannin kwamitin amintattu na ACF (BOT) da na gudanarwa ta NEC suka yanke shawarar dakatar da Mista Mamman Mike Osuman nan take.”

Sai dai Mista Osuman, ya yi zargin cewa ba a yi masa adalci ba wajen tsarin da aka bi na dakatar da shi.

An dai bayyana cewa, Mista Osuman ya tara tawagar manyan lauyoyin ne tun a karshen makon da ya gabata, a shirye-shiryen shigar da karar na kalubalantar dakatar da shi daga mukaminsa.

Wasu majiyoyi na kusa da shi sun ce ya tattara manyan lauyoyin Nijeriya guda takwas masu mukamin SANs da nufin kalubalantar dakatar da shi a kotu.

Bugu da kari, wasu majiyoyi na kusa da BoT da kuma NEC na kungiyar sun shaida cewa tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Alhaji Mahmud Yayale Ahmed ya kira taron masu ruwa da tsaki a ranar Talata a Abuja, inda suka tattauna kan bukatar gaggawa don magance rikicin wajen guje jefa ACF cikin wani babban rikicin siyasa.

An tattaro cewa, za a ci gaba da taron ne a ranar Asabar, yayin da karin shugabanni a yankin arewa ke kokarin ganin an shawo kan rikicin cikin gaggawa.

Ambasada Maisule ya bayyana kwarin gwiwa game da shirin sulhun, inda ya ce dattawan yankin sun dukufa wajen ganin an warware matsalar.

“Mutane suna yin kuskure a kowani lokaci, mu mutane ne amma kuskure ba za a taba sanya shi ba a matsayin daidai. Don haka dole ne a nemo mafita.

“Tattaunawa da cikakkun bayanai a bainar jama’a yanzu bai zama dole ba, saboda an riga an yi wani babban yunkuri na warware rikicin. Wadanda ke da hannu a cikin yunkurin suna da himma sosai kuma suna iya aikin.

“Na yi imani da iyawarsu na nemo hanyar warware matsalar, kuma ina da kyakkyawan fata game da sakamakon lamarin. A wurina, babban abu mai muhimmanci shi ne, kawar zargi tare da tallafa wa tsarin don tabbatar da ci gaba. A nan ne hankalina ya karkata,” in ji shi.

Arewa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
Tambarin Dimokuradiyya

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
Arewa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Next Post
Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

LABARAI MASU NASABA

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.