• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Sun Dukufa Wajen Warware Rikicin Siyasar Da Ta Kunno Kai A Kungiyar ACF

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dattawan Arewa Sun Dukufa Wajen Warware Rikicin Siyasar Da Ta Kunno Kai A Kungiyar ACF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu jiga-jigan masu fada a ji a yankin arewa sun shiga tsakani don warware rikicin siyasar da kunno kai bayan dakatarwar da shugaban kwamitin zartarwa na kungiyar Arewa ‘Consultatibe Forum’ (ACF), Mista Mamman Mike Osuman.

Mataimakin Shugaban Kwamitin Amintattu (BoT), Ambasada Ibrahim Maisule ne ya tabbatar da hakan a wata tattaunawa ta musamman a Abuja.

  •  Ali Nuhu Ya Zama Jakadan Kamfanin Tsaftace Haƙora A Arewacin Nijeriya 
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

A karshen makon da ya gabata ne dai aka dakatar da shugaban kwamitin zartarwa na kungiyar ACF bisa wasu kalamai da ya yi da suka shafi siyasa, wadanda kwamitin amintattu da wasu mambobin kungiyar suka yi watsi da su.

A cikin wata wasika tare da sa hannun babban sakataren kungiyar ACF, Malam Murtala Aliyu da shugabannin BoT, Alhaji Bashir Dalhatu, Mista Osuman, an zargi Mista Osuman da yin kalamai marasa izini da ke nuna cewa arewa za ta mara wa dan takarar shugaban kasa daga arewa baya a 2027.

Wasikar ta ci gaba da cewa, “An jawo hankalin kungiyar kan wasu bayanai da aka rika yadawa ga Mista Mamman Mike Osuman, SAN, OFR, Shugaban kwamitin zartarwa na ACF na kasa, wadanda aka yi a yayin taron kungiyar wanda aka yi a ranar Laraba, 20 ga Nuwamba, 2024, a hedkwatar ACF da ke Kaduna.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

“An ji Mista Osuman yana cewa arewa za ta mara wa dan takarar shugaban kasa daga arewa baya a 2027. Shugaban kungiyar ya yi wadannan kalamai ne ba tare da tuntuba ko tattaunawa da wasu shugabanni da mambobin kungiyar ta ACF ba, don haka ya nuna ra’ayinsa ne kwai.

“ACF ta yi watsi da kalaman Mista Mamman Mike Osuman gaba daya. Don haka ne shugabannin kwamitin amintattu na ACF (BOT) da na gudanarwa ta NEC suka yanke shawarar dakatar da Mista Mamman Mike Osuman nan take.”

Sai dai Mista Osuman, ya yi zargin cewa ba a yi masa adalci ba wajen tsarin da aka bi na dakatar da shi.

An dai bayyana cewa, Mista Osuman ya tara tawagar manyan lauyoyin ne tun a karshen makon da ya gabata, a shirye-shiryen shigar da karar na kalubalantar dakatar da shi daga mukaminsa.

Wasu majiyoyi na kusa da shi sun ce ya tattara manyan lauyoyin Nijeriya guda takwas masu mukamin SANs da nufin kalubalantar dakatar da shi a kotu.

Bugu da kari, wasu majiyoyi na kusa da BoT da kuma NEC na kungiyar sun shaida cewa tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Alhaji Mahmud Yayale Ahmed ya kira taron masu ruwa da tsaki a ranar Talata a Abuja, inda suka tattauna kan bukatar gaggawa don magance rikicin wajen guje jefa ACF cikin wani babban rikicin siyasa.

An tattaro cewa, za a ci gaba da taron ne a ranar Asabar, yayin da karin shugabanni a yankin arewa ke kokarin ganin an shawo kan rikicin cikin gaggawa.

Ambasada Maisule ya bayyana kwarin gwiwa game da shirin sulhun, inda ya ce dattawan yankin sun dukufa wajen ganin an warware matsalar.

“Mutane suna yin kuskure a kowani lokaci, mu mutane ne amma kuskure ba za a taba sanya shi ba a matsayin daidai. Don haka dole ne a nemo mafita.

“Tattaunawa da cikakkun bayanai a bainar jama’a yanzu bai zama dole ba, saboda an riga an yi wani babban yunkuri na warware rikicin. Wadanda ke da hannu a cikin yunkurin suna da himma sosai kuma suna iya aikin.

“Na yi imani da iyawarsu na nemo hanyar warware matsalar, kuma ina da kyakkyawan fata game da sakamakon lamarin. A wurina, babban abu mai muhimmanci shi ne, kawar zargi tare da tallafa wa tsarin don tabbatar da ci gaba. A nan ne hankalina ya karkata,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dattawan Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Abu Ya Sake Fashewa A Zamfara

Next Post

Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.