• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dauda Ya Kalubalanci Ganawar Sirri Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

by Hussein Yero
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi ƙwaƙƙwaran bincike kan sulhu da ake yi da ‘yan bindiga a Jihar Zamfara.

Rahotonni sun bayyana yadda wata tawaga ta gwamnatin tarayya take gudanar da zaman sulhu da ‘yan bindiga a Zamfara, ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

  • Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara
  • Sace Daliban Zamfara: Matawalle Ya Bayar Da Tabbacin Dawowarsu Cikin Koshin Lafiya

Mataimaki na musamman kan yada labarai na gwamna Dauda, Suleman Bala Idiris, ne ya bayyana haka a takardar da ya rabawa manema labarai a ranar Litinin.

A cewarsa gwamnatin Zamfara ta yi Allah wadai da tawagar da gwamnatin tarayya ke jagorantar wannan sulhu, ba tare da tuntuɓar gwamnatin jihar ba.

Kakakin gwamnan, ya ƙara da cewa, Gwamna Lawal, ya nemi Glgwamnatin tarayya da ta yi bincike tare da yin bayani kan wannan sulhu, domin yin hakan ya saɓa da matsayar da gwamnatinsa ta ɗauka tun da farko.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

Ya ce: “Gwamna Dauda Lawal yana neman ƙarin bayani daga gwamnatin tarayya kan sulhun da wasu waɗanda suka kira kansu wakilanta suke aiwatarwa a Jihar Zamfara.

“Gwamnatin Jihar Zamfara ta samu rahotanni cewa waɗannan wakilai na gwamnatin tarayya sun yi zaman sulhu da ‘yan bindiga a Birnin Magaji, Maradun, Mun Haye, Ajah, Bawo, da kuma Bagege.

“Sanin kowa ne, gwamnatocin baya da suka gabata a Jihar Zamfara sun jaraba yin sulhu da ‘yan bindiga, kuma abin bai haifar da ɗa mai ido ba.

“A dalilin haka ne gwamnatin Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta bayyana matsayarta tun farko cewa, babu ranar yin sulhu da ‘yan bindiga.

“Wannan matsaya ce da aka ɗauka domin tabbatar da an yaƙi wannan ɓarna gabaɗayanta. Kuma muna ganin nasarorin da ake samu ba ta hanyar yin sulhu ɗin ba. Muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta dakatar da wannan sulhu, domin ba alheri ba ne ga al’umman Jihar Zamfara.” Cewar sanar gwamnatin jihar ta bakin Sulaiman.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dauda LawalSulhuYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Garkuwa Da Kwamishinan Yada Labarai Na Jihar Benue

Next Post

Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

Related

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

51 minutes ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

1 hour ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

2 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

5 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

20 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

22 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami'ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.