• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dauda Ya Kalubalanci Ganawar Sirri Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

by Hussein Yero
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi ƙwaƙƙwaran bincike kan sulhu da ake yi da ‘yan bindiga a Jihar Zamfara.

Rahotonni sun bayyana yadda wata tawaga ta gwamnatin tarayya take gudanar da zaman sulhu da ‘yan bindiga a Zamfara, ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

  • Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara
  • Sace Daliban Zamfara: Matawalle Ya Bayar Da Tabbacin Dawowarsu Cikin Koshin Lafiya

Mataimaki na musamman kan yada labarai na gwamna Dauda, Suleman Bala Idiris, ne ya bayyana haka a takardar da ya rabawa manema labarai a ranar Litinin.

A cewarsa gwamnatin Zamfara ta yi Allah wadai da tawagar da gwamnatin tarayya ke jagorantar wannan sulhu, ba tare da tuntuɓar gwamnatin jihar ba.

Kakakin gwamnan, ya ƙara da cewa, Gwamna Lawal, ya nemi Glgwamnatin tarayya da ta yi bincike tare da yin bayani kan wannan sulhu, domin yin hakan ya saɓa da matsayar da gwamnatinsa ta ɗauka tun da farko.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Ya ce: “Gwamna Dauda Lawal yana neman ƙarin bayani daga gwamnatin tarayya kan sulhun da wasu waɗanda suka kira kansu wakilanta suke aiwatarwa a Jihar Zamfara.

“Gwamnatin Jihar Zamfara ta samu rahotanni cewa waɗannan wakilai na gwamnatin tarayya sun yi zaman sulhu da ‘yan bindiga a Birnin Magaji, Maradun, Mun Haye, Ajah, Bawo, da kuma Bagege.

“Sanin kowa ne, gwamnatocin baya da suka gabata a Jihar Zamfara sun jaraba yin sulhu da ‘yan bindiga, kuma abin bai haifar da ɗa mai ido ba.

“A dalilin haka ne gwamnatin Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta bayyana matsayarta tun farko cewa, babu ranar yin sulhu da ‘yan bindiga.

“Wannan matsaya ce da aka ɗauka domin tabbatar da an yaƙi wannan ɓarna gabaɗayanta. Kuma muna ganin nasarorin da ake samu ba ta hanyar yin sulhu ɗin ba. Muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta dakatar da wannan sulhu, domin ba alheri ba ne ga al’umman Jihar Zamfara.” Cewar sanar gwamnatin jihar ta bakin Sulaiman.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dauda LawalSulhuYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Garkuwa Da Kwamishinan Yada Labarai Na Jihar Benue

Next Post

Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

Related

Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

8 hours ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

11 hours ago
An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
Manyan Labarai

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

15 hours ago
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

17 hours ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

18 hours ago
Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

1 day ago
Next Post
Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami'ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.