ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dauda Ya Kalubalanci Ganawar Sirri Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

by Hussein Yero
3 years ago
Zamfara

Gwamna Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi ƙwaƙƙwaran bincike kan sulhu da ake yi da ‘yan bindiga a Jihar Zamfara.

Rahotonni sun bayyana yadda wata tawaga ta gwamnatin tarayya take gudanar da zaman sulhu da ‘yan bindiga a Zamfara, ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

  • Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara
  • Sace Daliban Zamfara: Matawalle Ya Bayar Da Tabbacin Dawowarsu Cikin Koshin Lafiya

Mataimaki na musamman kan yada labarai na gwamna Dauda, Suleman Bala Idiris, ne ya bayyana haka a takardar da ya rabawa manema labarai a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

A cewarsa gwamnatin Zamfara ta yi Allah wadai da tawagar da gwamnatin tarayya ke jagorantar wannan sulhu, ba tare da tuntuɓar gwamnatin jihar ba.

Kakakin gwamnan, ya ƙara da cewa, Gwamna Lawal, ya nemi Glgwamnatin tarayya da ta yi bincike tare da yin bayani kan wannan sulhu, domin yin hakan ya saɓa da matsayar da gwamnatinsa ta ɗauka tun da farko.

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Ya ce: “Gwamna Dauda Lawal yana neman ƙarin bayani daga gwamnatin tarayya kan sulhun da wasu waɗanda suka kira kansu wakilanta suke aiwatarwa a Jihar Zamfara.

“Gwamnatin Jihar Zamfara ta samu rahotanni cewa waɗannan wakilai na gwamnatin tarayya sun yi zaman sulhu da ‘yan bindiga a Birnin Magaji, Maradun, Mun Haye, Ajah, Bawo, da kuma Bagege.

“Sanin kowa ne, gwamnatocin baya da suka gabata a Jihar Zamfara sun jaraba yin sulhu da ‘yan bindiga, kuma abin bai haifar da ɗa mai ido ba.

“A dalilin haka ne gwamnatin Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta bayyana matsayarta tun farko cewa, babu ranar yin sulhu da ‘yan bindiga.

“Wannan matsaya ce da aka ɗauka domin tabbatar da an yaƙi wannan ɓarna gabaɗayanta. Kuma muna ganin nasarorin da ake samu ba ta hanyar yin sulhu ɗin ba. Muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta dakatar da wannan sulhu, domin ba alheri ba ne ga al’umman Jihar Zamfara.” Cewar sanar gwamnatin jihar ta bakin Sulaiman.

Zamfara
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
Next Post
Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami'ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.