• Leadership Hausa
Saturday, December 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dauda Ya Kalubalanci Ganawar Sirri Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

by Hussein Yero
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi ƙwaƙƙwaran bincike kan sulhu da ake yi da ‘yan bindiga a Jihar Zamfara.

Rahotonni sun bayyana yadda wata tawaga ta gwamnatin tarayya take gudanar da zaman sulhu da ‘yan bindiga a Zamfara, ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

  • Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara
  • Sace Daliban Zamfara: Matawalle Ya Bayar Da Tabbacin Dawowarsu Cikin Koshin Lafiya

Mataimaki na musamman kan yada labarai na gwamna Dauda, Suleman Bala Idiris, ne ya bayyana haka a takardar da ya rabawa manema labarai a ranar Litinin.

A cewarsa gwamnatin Zamfara ta yi Allah wadai da tawagar da gwamnatin tarayya ke jagorantar wannan sulhu, ba tare da tuntuɓar gwamnatin jihar ba.

Kakakin gwamnan, ya ƙara da cewa, Gwamna Lawal, ya nemi Glgwamnatin tarayya da ta yi bincike tare da yin bayani kan wannan sulhu, domin yin hakan ya saɓa da matsayar da gwamnatinsa ta ɗauka tun da farko.

Labarai Masu Nasaba

CBN Zai Haramta Harkokin Kudi A Asusun Bankin Da Babu BVN Da NIN A 2024

Zaben Kano: Alkali Na Fuskantar Tuhuma Kan Kuskuren Da Aka Tafka

Ya ce: “Gwamna Dauda Lawal yana neman ƙarin bayani daga gwamnatin tarayya kan sulhun da wasu waɗanda suka kira kansu wakilanta suke aiwatarwa a Jihar Zamfara.

“Gwamnatin Jihar Zamfara ta samu rahotanni cewa waɗannan wakilai na gwamnatin tarayya sun yi zaman sulhu da ‘yan bindiga a Birnin Magaji, Maradun, Mun Haye, Ajah, Bawo, da kuma Bagege.

“Sanin kowa ne, gwamnatocin baya da suka gabata a Jihar Zamfara sun jaraba yin sulhu da ‘yan bindiga, kuma abin bai haifar da ɗa mai ido ba.

“A dalilin haka ne gwamnatin Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta bayyana matsayarta tun farko cewa, babu ranar yin sulhu da ‘yan bindiga.

“Wannan matsaya ce da aka ɗauka domin tabbatar da an yaƙi wannan ɓarna gabaɗayanta. Kuma muna ganin nasarorin da ake samu ba ta hanyar yin sulhu ɗin ba. Muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta dakatar da wannan sulhu, domin ba alheri ba ne ga al’umman Jihar Zamfara.” Cewar sanar gwamnatin jihar ta bakin Sulaiman.

Tags: Dauda LawalSulhuYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Garkuwa Da Kwamishinan Yada Labarai Na Jihar Benue

Next Post

Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

Related

CBN Zai Haramta Harkokin Kudi A Asusun Bankin Da Babu BVN Da NIN A 2024
Manyan Labarai

CBN Zai Haramta Harkokin Kudi A Asusun Bankin Da Babu BVN Da NIN A 2024

21 hours ago
Zaben Kano: Alkali Na Fuskantar Tuhuma Kan Kuskuren Da Aka Tafka
Manyan Labarai

Zaben Kano: Alkali Na Fuskantar Tuhuma Kan Kuskuren Da Aka Tafka

1 day ago
Shari’ar Zaben Gwamnoni: Kallo Ya Koma Kotun Koli
Manyan Labarai

Shari’ar Zaben Gwamnoni: Kallo Ya Koma Kotun Koli

1 day ago
Lallai A Rika Hukunta Masu Aikata Laifukan Zabe
Manyan Labarai

Lallai A Rika Hukunta Masu Aikata Laifukan Zabe

1 day ago
Ba Sai Da Yawan Kuri’u Kadai Ake Lashe Zabe Ba – Doguwa
Manyan Labarai

Ba Sai Da Yawan Kuri’u Kadai Ake Lashe Zabe Ba – Doguwa

2 days ago
Kwace Wa NNPP Zaben Kano Na Iya Haddasa Tashin Hankali A Afrika – NNPP
Manyan Labarai

Kwace Wa NNPP Zaben Kano Na Iya Haddasa Tashin Hankali A Afrika – NNPP

2 days ago
Next Post
Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami'ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Tare Da Dukkan Bangarori Don Gina Duniya Mai Tsabta

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Tare Da Dukkan Bangarori Don Gina Duniya Mai Tsabta

December 2, 2023
An Kori Jaruma Daga Fim Saboda Wallafa Sakon Goyon Bayan Falasdinawa

An Kori Jaruma Daga Fim Saboda Wallafa Sakon Goyon Bayan Falasdinawa

December 2, 2023
Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

December 2, 2023
Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma

Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma

December 2, 2023
Gwamnatin Tarayya Za Ta Samar Da Kundin Tattara Bayanai Na Ilimi

Gwamnatin Tarayya Za Ta Samar Da Kundin Tattara Bayanai Na Ilimi

December 2, 2023
Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

December 2, 2023
Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana

Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana

December 2, 2023
Tsaka Mai Wuyar Da Masu Gidajen Burodi Ke Ciki A Kaduna – Yarima

Tsaka Mai Wuyar Da Masu Gidajen Burodi Ke Ciki A Kaduna – Yarima

December 2, 2023
Gwamnatin Legas Za Ta Yi Amfani Da Fasaha Don Magance Matsalolin Cikin Gida

Gwamnatin Legas Za Ta Yi Amfani Da Fasaha Don Magance Matsalolin Cikin Gida

December 2, 2023
Shirin NPA Na Kula Da Tashoshin Jiragen Ruwa A Dunkule Zai Bunkasa Tattalin Arzikin Cikin Teku

Shirin NPA Na Kula Da Tashoshin Jiragen Ruwa A Dunkule Zai Bunkasa Tattalin Arzikin Cikin Teku

December 2, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.