• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

by Sadiq
4 hours ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitaccen ɗan jaridar nan kuma mawallafin mujallar Ovation, Dele Momodu, ya bayyana cewa ya fice daga Jam’iyyar PDP tare da komawa jam’iyyar ADC.

A cikin wata wasiƙar da ya rubuta a ranar 17 ga watan Yuli, 2025, wacce ya aike wa Shugaban PDP na mazaɓar Ihievbe, ƙaramar hukumar Owan East ta Jihar Edo.

  • Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara
  • Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Momodu ya ce ya fice daga jam’iyyar ne saboda ta faɗa hannun masu adawa da dimokuraɗiyya.

Ya bayyana cewa yanzu zai mara wa jam’iyyar  ADC baya, wacce ke son ƙwace mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

“Ina sanar da ku cewa na fice daga jam’iyyar PDP daga yau,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

“Dalilina kuwa yana da sauƙi. Jam’iyyar ta faɗa hannun masu adawa da dimokuraɗiyya.

“Saboda haka, abin da ya dace shi ne a bar musu ragowar jam’iyyar, yayin da mu da yawa za mu koma sabuwar jam’iyyar haɗaka mai suna ADC.”

A farkon wannan wata, Momodu ya zargi Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da yi wa jam’iyyar APC aiki a ɓoye duk da kasancewarsa ɗan jam’iyyar PDP a lokacin zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Ya ce: “Ba tare da wata shakka ba, mutane suna bar wa Wike da abokan aikinsa PDP. Wannan lamari an riga an hango shi. Jam’iyyar APC mai mulki tana shigar da mutanenta a manyan jam’iyyun adawa don tarwatsa su.”

Haka kuma, Momodu ya caccaki gwamnatin Bola Tinubu, yana cewa tana ƙara jefa rayuwar ‘yan Nijeriya cikin ƙunci fiye da yadda aka gani a lokacin tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.

“Shin wannan ita ce Nijeriya da kuke mafarki? Rayuwarku ta fi ta da sauƙi ne fiye da shekaru biyu da suka wuce? Ko da Buhari ya tafi, mun ga abin da ya bari, amma yanzu lamarin ya ƙara muni,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCDele MomoduPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Next Post

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

7 hours ago
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
Manyan Labarai

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

9 hours ago
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu
Manyan Labarai

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

10 hours ago
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde
Labarai

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

21 hours ago
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

1 day ago
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya
Manyan Labarai

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

1 day ago
Next Post
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

July 17, 2025
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

July 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

July 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

July 17, 2025
Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

July 17, 2025
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

July 17, 2025
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.