• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Kama ‘Yan Ta’adda 3 A Kaduna Da Kano

bySadiq
2 years ago
DSS

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta ce jami’anta da sauran ‘yan uwanta, a ranar Litinin din da ta gabata, sun kai samame maboyar ‘yan ta’adda a jihohin Kaduna da Kano, inda suka cafke wasu mutum uku.

Wadanda ake zargin sun yi amfani da abubuwa masu fashewa kan jami’an tsaro da suka hada da sojojin Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyen Filato
  • Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Kakakin hukumar tsaro ta farin kaya DSS, Dokta Peter Afunanya, ya bayyana cewa, a yayin farmakin da suka kai Jihar Kaduna, ‘yan ta’addan sun baza makamai masu guba a kan jami’an tsaro da ke yaki da su.

Ya ce: “Dakarun sojojin Nijeriya da na ‘yan sanda, a safiyar ranar 15 ga watan Mayu, 2023 a lokaci guda sun kai farmaki maboyar ‘yan ta’adda a sassan Kaduna da Kano.

“A yayin farmakin da suka kai jihar Kaduna, ‘yan ta’addan sun jefa wa jami’an tsaro bama-bamai.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

“Daya daga cikin ‘yan ta’addan da ya sanya rigar kunar bakin wake ya tarwatsa kansa. Yayin da aka kama wasu mutane uku da ake zargi.

“Abubuwan da aka gano a wani bincike da aka yi a maboyarsu, an samu rigar din kunar bakin wake guda biyu, bindiga AK-47 daya da kuma bindigar tafi-da-gidanka guda daya.”

A halin da ake ciki kuma, a Jihar Kano, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce an kama mutane biyu a yayin da aka kwato kayayyakin da suka hada da bindiga, wayoyin hannu 11, gurneti guda biyu, AK-47 guda biyu, mota kirar Peugeot 307 daya da katin shaida mallakin wanda ake zargi da tserewa.

“Da farko dai bayanan sirri sun nuna cewa manyan ‘yan ta’adda na sake haduwa a yankin Arewa maso Yamma domin aiwatar da munanan ayyuka a yankin, musamman yadda ayyukan soji ke ci gaba da yi a yankin Arewa maso Gabas ya sanya ‘yan ta’addan tserewa zuwa shiyyar Arewa maso Yamma.

“Hukumar ta yaba wa sojojin Nijeriya da ‘yan sandan Nijeriya bisa jajircewa da goyon bayan da suka bayar wanda ya kai ga samun nasarar aikin, ci gaba da hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, ba tare da wata shakka ba, wani canji ne wajen daukar matakan dakile barazanar.

“Har ila yau, Hukumar na fatan bayyana karara cewa, za ta ci gaba da hada kai da ‘yan’uwa hukumomin domin kawar da miyagun laifuka musamman a wannan lokaci na mika mulki da ma bayan mika mulki, “in ji Afunanya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version