ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Kama ‘Yan Ta’adda 3 A Kaduna Da Kano

by Sadiq
3 years ago
DSS

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta ce jami’anta da sauran ‘yan uwanta, a ranar Litinin din da ta gabata, sun kai samame maboyar ‘yan ta’adda a jihohin Kaduna da Kano, inda suka cafke wasu mutum uku.

Wadanda ake zargin sun yi amfani da abubuwa masu fashewa kan jami’an tsaro da suka hada da sojojin Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyen Filato
  • Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Kakakin hukumar tsaro ta farin kaya DSS, Dokta Peter Afunanya, ya bayyana cewa, a yayin farmakin da suka kai Jihar Kaduna, ‘yan ta’addan sun baza makamai masu guba a kan jami’an tsaro da ke yaki da su.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Dakarun sojojin Nijeriya da na ‘yan sanda, a safiyar ranar 15 ga watan Mayu, 2023 a lokaci guda sun kai farmaki maboyar ‘yan ta’adda a sassan Kaduna da Kano.

“A yayin farmakin da suka kai jihar Kaduna, ‘yan ta’addan sun jefa wa jami’an tsaro bama-bamai.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Daya daga cikin ‘yan ta’addan da ya sanya rigar kunar bakin wake ya tarwatsa kansa. Yayin da aka kama wasu mutane uku da ake zargi.

“Abubuwan da aka gano a wani bincike da aka yi a maboyarsu, an samu rigar din kunar bakin wake guda biyu, bindiga AK-47 daya da kuma bindigar tafi-da-gidanka guda daya.”

A halin da ake ciki kuma, a Jihar Kano, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce an kama mutane biyu a yayin da aka kwato kayayyakin da suka hada da bindiga, wayoyin hannu 11, gurneti guda biyu, AK-47 guda biyu, mota kirar Peugeot 307 daya da katin shaida mallakin wanda ake zargi da tserewa.

“Da farko dai bayanan sirri sun nuna cewa manyan ‘yan ta’adda na sake haduwa a yankin Arewa maso Yamma domin aiwatar da munanan ayyuka a yankin, musamman yadda ayyukan soji ke ci gaba da yi a yankin Arewa maso Gabas ya sanya ‘yan ta’addan tserewa zuwa shiyyar Arewa maso Yamma.

“Hukumar ta yaba wa sojojin Nijeriya da ‘yan sandan Nijeriya bisa jajircewa da goyon bayan da suka bayar wanda ya kai ga samun nasarar aikin, ci gaba da hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, ba tare da wata shakka ba, wani canji ne wajen daukar matakan dakile barazanar.

“Har ila yau, Hukumar na fatan bayyana karara cewa, za ta ci gaba da hada kai da ‘yan’uwa hukumomin domin kawar da miyagun laifuka musamman a wannan lokaci na mika mulki da ma bayan mika mulki, “in ji Afunanya.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.