ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Kama ‘Yan Ta’adda 3 A Kaduna Da Kano

by Sadiq
3 years ago
DSS

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta ce jami’anta da sauran ‘yan uwanta, a ranar Litinin din da ta gabata, sun kai samame maboyar ‘yan ta’adda a jihohin Kaduna da Kano, inda suka cafke wasu mutum uku.

Wadanda ake zargin sun yi amfani da abubuwa masu fashewa kan jami’an tsaro da suka hada da sojojin Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyen Filato
  • Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Kakakin hukumar tsaro ta farin kaya DSS, Dokta Peter Afunanya, ya bayyana cewa, a yayin farmakin da suka kai Jihar Kaduna, ‘yan ta’addan sun baza makamai masu guba a kan jami’an tsaro da ke yaki da su.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Dakarun sojojin Nijeriya da na ‘yan sanda, a safiyar ranar 15 ga watan Mayu, 2023 a lokaci guda sun kai farmaki maboyar ‘yan ta’adda a sassan Kaduna da Kano.

“A yayin farmakin da suka kai jihar Kaduna, ‘yan ta’addan sun jefa wa jami’an tsaro bama-bamai.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Daya daga cikin ‘yan ta’addan da ya sanya rigar kunar bakin wake ya tarwatsa kansa. Yayin da aka kama wasu mutane uku da ake zargi.

“Abubuwan da aka gano a wani bincike da aka yi a maboyarsu, an samu rigar din kunar bakin wake guda biyu, bindiga AK-47 daya da kuma bindigar tafi-da-gidanka guda daya.”

A halin da ake ciki kuma, a Jihar Kano, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce an kama mutane biyu a yayin da aka kwato kayayyakin da suka hada da bindiga, wayoyin hannu 11, gurneti guda biyu, AK-47 guda biyu, mota kirar Peugeot 307 daya da katin shaida mallakin wanda ake zargi da tserewa.

“Da farko dai bayanan sirri sun nuna cewa manyan ‘yan ta’adda na sake haduwa a yankin Arewa maso Yamma domin aiwatar da munanan ayyuka a yankin, musamman yadda ayyukan soji ke ci gaba da yi a yankin Arewa maso Gabas ya sanya ‘yan ta’addan tserewa zuwa shiyyar Arewa maso Yamma.

“Hukumar ta yaba wa sojojin Nijeriya da ‘yan sandan Nijeriya bisa jajircewa da goyon bayan da suka bayar wanda ya kai ga samun nasarar aikin, ci gaba da hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, ba tare da wata shakka ba, wani canji ne wajen daukar matakan dakile barazanar.

“Har ila yau, Hukumar na fatan bayyana karara cewa, za ta ci gaba da hada kai da ‘yan’uwa hukumomin domin kawar da miyagun laifuka musamman a wannan lokaci na mika mulki da ma bayan mika mulki, “in ji Afunanya.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.