ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Kama ‘Yan Ta’adda 3 A Kaduna Da Kano

by Sadiq
3 years ago
DSS

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta ce jami’anta da sauran ‘yan uwanta, a ranar Litinin din da ta gabata, sun kai samame maboyar ‘yan ta’adda a jihohin Kaduna da Kano, inda suka cafke wasu mutum uku.

Wadanda ake zargin sun yi amfani da abubuwa masu fashewa kan jami’an tsaro da suka hada da sojojin Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyen Filato
  • Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Kakakin hukumar tsaro ta farin kaya DSS, Dokta Peter Afunanya, ya bayyana cewa, a yayin farmakin da suka kai Jihar Kaduna, ‘yan ta’addan sun baza makamai masu guba a kan jami’an tsaro da ke yaki da su.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Dakarun sojojin Nijeriya da na ‘yan sanda, a safiyar ranar 15 ga watan Mayu, 2023 a lokaci guda sun kai farmaki maboyar ‘yan ta’adda a sassan Kaduna da Kano.

“A yayin farmakin da suka kai jihar Kaduna, ‘yan ta’addan sun jefa wa jami’an tsaro bama-bamai.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

“Daya daga cikin ‘yan ta’addan da ya sanya rigar kunar bakin wake ya tarwatsa kansa. Yayin da aka kama wasu mutane uku da ake zargi.

“Abubuwan da aka gano a wani bincike da aka yi a maboyarsu, an samu rigar din kunar bakin wake guda biyu, bindiga AK-47 daya da kuma bindigar tafi-da-gidanka guda daya.”

A halin da ake ciki kuma, a Jihar Kano, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce an kama mutane biyu a yayin da aka kwato kayayyakin da suka hada da bindiga, wayoyin hannu 11, gurneti guda biyu, AK-47 guda biyu, mota kirar Peugeot 307 daya da katin shaida mallakin wanda ake zargi da tserewa.

“Da farko dai bayanan sirri sun nuna cewa manyan ‘yan ta’adda na sake haduwa a yankin Arewa maso Yamma domin aiwatar da munanan ayyuka a yankin, musamman yadda ayyukan soji ke ci gaba da yi a yankin Arewa maso Gabas ya sanya ‘yan ta’addan tserewa zuwa shiyyar Arewa maso Yamma.

“Hukumar ta yaba wa sojojin Nijeriya da ‘yan sandan Nijeriya bisa jajircewa da goyon bayan da suka bayar wanda ya kai ga samun nasarar aikin, ci gaba da hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, ba tare da wata shakka ba, wani canji ne wajen daukar matakan dakile barazanar.

“Har ila yau, Hukumar na fatan bayyana karara cewa, za ta ci gaba da hada kai da ‘yan’uwa hukumomin domin kawar da miyagun laifuka musamman a wannan lokaci na mika mulki da ma bayan mika mulki, “in ji Afunanya.

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.