ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubban Manoma Za Su Amfana Da Fasahar Adana Tumatir A Kano

by Abubakar Abba
3 years ago
Manoma

Kimanin manonan tumatir dubu uku da ke Jihar Kano, za su amfana da fasahar adana tumatir a karkashin shirin da wata kungiya mai zaman kanta, mai suna ‘Pydera Global YieldWise Nigeria’ ta kirkiro da shi.

Kungiyar ta fito da shirin ne don rage wa manoman na tumatir da ke jihar yawan asarar da suke yi, a kasuwar tumatirin din.

  • Dimbin Ribar Noman Inabi A Nijeriya

Aikin, wanda kuma gidauniyar Rockefeller ce ta samar da kudi don yinsa, an kirkiro da shi ne don magance asarar da manoman na tumatir suke yi a lokacin da suka dasa shi da kuma kan sauran amfanin gona da ake shuka wa a kasar nan.

ADVERTISEMENT

Daraktan shirin Lekan Tobi ne ya sanar da hakan a lokacin kaddamar da shirin a kauyen Kwanar Agalawa da ke cikin karamar hukumar Garunmalam da ke jihar ta Kano a ranar Talatar da ta wuce.

Kamfanin dillancin labarai na kasa, ya ruwaito cewar, kauyen na Kwanar Agalawa, yana daya daga cikin yankunan da ake noma tumatir mai yawa a jihar.
A cewar Mista Tobi, kungiyar ta yanke shawarar kirkiro da aikin ne don shawo kan kalubalen da manoman suke fuskan ta ne a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

Ya ci gaba da cewa, manoman tumatir su dubu uku da aka zabo daga cikin kungiyoyin manoma arba’in da hudu ne za su amfana da shirin, inda za a samar musu da wajen adana tumatir da kuma sarrafa shi.

Ya bayyana cewar, manoman suna da zabin samo musu sayen tumatir din su da kuma samun ingantaccen irin tumatir don samun yin noma mai riba.
Ya yi nuni da cewa, a bisa fasahar, za kuma a koyawa manoman yadda za su adana Kokumba da Albasa da Shinkafa da masara da sauransu.

Shi kuwa a nasa jawabain a wurin taron, Mataimakin gwamnan jihar Kano Alhaji Nasiru Gawuna, ya ce gwamnatin jihar zata ci gaba da baiwa fannin aikin gona fifiko, musamman don samar da wadataccen abinci a jihar.

Mataimakin gwamnan wanda babban sakatatare a ma’aikatar aikin gona da albarkantu na jihar Aminu Garba ya wakilce shi a wurin taron mataimakin gwamnan ya kuma ya ba a kan kirkiro da shirin na YieldWise Nijeriya.

Taron ya kuma samu halartar masu noma tumatir da sauran masu ruwa da tsaki a fannin, harda wakilan da suka fito daga jihar Jigawa da Katsina da Kaduna da kuma Folato.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
Yadda Ridi Da Kwai Ke Gyara Jikin Mace (2)

Yadda Ridi Da Kwai Ke Gyara Jikin Mace (2)

LABARAI MASU NASABA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.