ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Yi Aiki Da Manhajoji Domin Tantance Kwazon Ministoci

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Manhajoji

Gwamnatin tarayya ta cimma wasu matakai da ministoci za su gabatar da kwazonsu da suka iya cimmawa a ma’aikatunsu daban-daban, hakan kuma na cikin muhimman bangarori takwas da Shugaban kasa, Bola Tinubu ya sanya a gabasa.

Babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan manufofi da tsare-tsare, Hajiya Hadiza Bala-Usman ce ta sanar da hakan a Abuja cikin makon nan.

  • Sin: An Fitar Da Tsarin Tallafin Kudade Domin Bunkasa Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku

Shugaban kasa ya shaida wa ministocinsa cewa tilas a kowace bayan wata uku su gabatar da kwazonsu domin sanin irin azama ko akasinsa da suke yi a bakin aikinsu.

ADVERTISEMENT

Kazalika, gwamnatin Tinubu ta tsara da fitar da wani manhaja da zai bibiyar kwazon ministoci a ma’aikatunsu, manhajar mai suna ‘Citizens’ Delibery Tracker App’.

‘Yan Nijeriya za su iya amfani da manhajar wajen bayar da bayani ko ra’ayinsu kan manufofi da tsare-tsaren da gwamnati ke musu.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Sannan, hatta ayyukan mazabu da ake bai wa sanatoci da ‘yan majalisu za a dunga bibiya ta wannan manhajar.

Hadiza ta jaddada aniyar gwamnatin Tinubu na gudanar da gwamnati mai cike da gaskiya da fayyace komai ga al’umman kasa.

Ta ce, shugaban kasa ya umarci dukkanin ministoci da dunga zama da al’umman mazabun sanatocin yankunansu a kowace zango na bayan wata uku.

Ta take bayyana sabuwar salon mulkin Tinubu mai suna “Tsarin Mulki Na ‘Yan Kasa”, Hadiza ta ce, tun da dai ministocin nan sun rattaba hannun kan yarjejeniyar yin aiki tukuru, dole ne za a bibiyesu da tantancesu kan muhimman ajandoji guda takwas na Tinubu.

A cewarta, da wannan sabon dabarar bibiyar aikin za a samu cimma muhimman nasarori kan bangarori guda takwas da shugaban kasa ya sanya a gaba wajen ganin ya aiwatar domin kyautata rayuwar al’ummar Nijeriya.

A fadinta kuma, Tinubu ya amince al’umman Nijeriya su san dukkanin abubuwan da gwamnati ke yi da samun damar mu’amalar kai tsaye da ministoci domin himmar da yake da shi wajen gudanar da shugabanci na kwarai ga al’umman kasa.

Ta kara da cewa, sun kuma fito da tsarin gabatar da rahoton ayyuka da zai ba da dama ake samun hakikanin rahotonnin ayyuka da kwazon kowace ma’aikata da rassan gwamnati da kuma hukumominta.

“Muna rungumar tsarin gudanarwa ne na kasa da kasa domin kyautata shugabanci ta hanyar ganowa da bibiyar kwazon ma’aikatu a bangaren aiwatar da manufofi da tsare-tsaren gwamnati,” ta shaida.

Hadiza ta ce jama’an kasa za su iya samun manhajar bibiyar ayyukan da kwazon ne ta shafin yanar gizo kamar haka: app.cdcu.gob.ng.

Ta ce nan da wata guda za a dora manhajar a turakar ‘Google Play Store’ da ‘Apple store’, manhajar zai ba da dama jama’a su san masu kokari da akasin haka.

   

Manhajoji
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.