ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Yi Aiki Da Manhajoji Domin Tantance Kwazon Ministoci

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Manhajoji

Gwamnatin tarayya ta cimma wasu matakai da ministoci za su gabatar da kwazonsu da suka iya cimmawa a ma’aikatunsu daban-daban, hakan kuma na cikin muhimman bangarori takwas da Shugaban kasa, Bola Tinubu ya sanya a gabasa.

Babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan manufofi da tsare-tsare, Hajiya Hadiza Bala-Usman ce ta sanar da hakan a Abuja cikin makon nan.

  • Sin: An Fitar Da Tsarin Tallafin Kudade Domin Bunkasa Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku

Shugaban kasa ya shaida wa ministocinsa cewa tilas a kowace bayan wata uku su gabatar da kwazonsu domin sanin irin azama ko akasinsa da suke yi a bakin aikinsu.

ADVERTISEMENT

Kazalika, gwamnatin Tinubu ta tsara da fitar da wani manhaja da zai bibiyar kwazon ministoci a ma’aikatunsu, manhajar mai suna ‘Citizens’ Delibery Tracker App’.

‘Yan Nijeriya za su iya amfani da manhajar wajen bayar da bayani ko ra’ayinsu kan manufofi da tsare-tsaren da gwamnati ke musu.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Sannan, hatta ayyukan mazabu da ake bai wa sanatoci da ‘yan majalisu za a dunga bibiya ta wannan manhajar.

Hadiza ta jaddada aniyar gwamnatin Tinubu na gudanar da gwamnati mai cike da gaskiya da fayyace komai ga al’umman kasa.

Ta ce, shugaban kasa ya umarci dukkanin ministoci da dunga zama da al’umman mazabun sanatocin yankunansu a kowace zango na bayan wata uku.

Ta take bayyana sabuwar salon mulkin Tinubu mai suna “Tsarin Mulki Na ‘Yan Kasa”, Hadiza ta ce, tun da dai ministocin nan sun rattaba hannun kan yarjejeniyar yin aiki tukuru, dole ne za a bibiyesu da tantancesu kan muhimman ajandoji guda takwas na Tinubu.

A cewarta, da wannan sabon dabarar bibiyar aikin za a samu cimma muhimman nasarori kan bangarori guda takwas da shugaban kasa ya sanya a gaba wajen ganin ya aiwatar domin kyautata rayuwar al’ummar Nijeriya.

A fadinta kuma, Tinubu ya amince al’umman Nijeriya su san dukkanin abubuwan da gwamnati ke yi da samun damar mu’amalar kai tsaye da ministoci domin himmar da yake da shi wajen gudanar da shugabanci na kwarai ga al’umman kasa.

Ta kara da cewa, sun kuma fito da tsarin gabatar da rahoton ayyuka da zai ba da dama ake samun hakikanin rahotonnin ayyuka da kwazon kowace ma’aikata da rassan gwamnati da kuma hukumominta.

“Muna rungumar tsarin gudanarwa ne na kasa da kasa domin kyautata shugabanci ta hanyar ganowa da bibiyar kwazon ma’aikatu a bangaren aiwatar da manufofi da tsare-tsaren gwamnati,” ta shaida.

Hadiza ta ce jama’an kasa za su iya samun manhajar bibiyar ayyukan da kwazon ne ta shafin yanar gizo kamar haka: app.cdcu.gob.ng.

Ta ce nan da wata guda za a dora manhajar a turakar ‘Google Play Store’ da ‘Apple store’, manhajar zai ba da dama jama’a su san masu kokari da akasin haka.

   

Manhajoji
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.