ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Yi Aiki Da Manhajoji Domin Tantance Kwazon Ministoci

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Manhajoji

Gwamnatin tarayya ta cimma wasu matakai da ministoci za su gabatar da kwazonsu da suka iya cimmawa a ma’aikatunsu daban-daban, hakan kuma na cikin muhimman bangarori takwas da Shugaban kasa, Bola Tinubu ya sanya a gabasa.

Babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan manufofi da tsare-tsare, Hajiya Hadiza Bala-Usman ce ta sanar da hakan a Abuja cikin makon nan.

  • Sin: An Fitar Da Tsarin Tallafin Kudade Domin Bunkasa Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku

Shugaban kasa ya shaida wa ministocinsa cewa tilas a kowace bayan wata uku su gabatar da kwazonsu domin sanin irin azama ko akasinsa da suke yi a bakin aikinsu.

ADVERTISEMENT

Kazalika, gwamnatin Tinubu ta tsara da fitar da wani manhaja da zai bibiyar kwazon ministoci a ma’aikatunsu, manhajar mai suna ‘Citizens’ Delibery Tracker App’.

‘Yan Nijeriya za su iya amfani da manhajar wajen bayar da bayani ko ra’ayinsu kan manufofi da tsare-tsaren da gwamnati ke musu.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Sannan, hatta ayyukan mazabu da ake bai wa sanatoci da ‘yan majalisu za a dunga bibiya ta wannan manhajar.

Hadiza ta jaddada aniyar gwamnatin Tinubu na gudanar da gwamnati mai cike da gaskiya da fayyace komai ga al’umman kasa.

Ta ce, shugaban kasa ya umarci dukkanin ministoci da dunga zama da al’umman mazabun sanatocin yankunansu a kowace zango na bayan wata uku.

Ta take bayyana sabuwar salon mulkin Tinubu mai suna “Tsarin Mulki Na ‘Yan Kasa”, Hadiza ta ce, tun da dai ministocin nan sun rattaba hannun kan yarjejeniyar yin aiki tukuru, dole ne za a bibiyesu da tantancesu kan muhimman ajandoji guda takwas na Tinubu.

A cewarta, da wannan sabon dabarar bibiyar aikin za a samu cimma muhimman nasarori kan bangarori guda takwas da shugaban kasa ya sanya a gaba wajen ganin ya aiwatar domin kyautata rayuwar al’ummar Nijeriya.

A fadinta kuma, Tinubu ya amince al’umman Nijeriya su san dukkanin abubuwan da gwamnati ke yi da samun damar mu’amalar kai tsaye da ministoci domin himmar da yake da shi wajen gudanar da shugabanci na kwarai ga al’umman kasa.

Ta kara da cewa, sun kuma fito da tsarin gabatar da rahoton ayyuka da zai ba da dama ake samun hakikanin rahotonnin ayyuka da kwazon kowace ma’aikata da rassan gwamnati da kuma hukumominta.

“Muna rungumar tsarin gudanarwa ne na kasa da kasa domin kyautata shugabanci ta hanyar ganowa da bibiyar kwazon ma’aikatu a bangaren aiwatar da manufofi da tsare-tsaren gwamnati,” ta shaida.

Hadiza ta ce jama’an kasa za su iya samun manhajar bibiyar ayyukan da kwazon ne ta shafin yanar gizo kamar haka: app.cdcu.gob.ng.

Ta ce nan da wata guda za a dora manhajar a turakar ‘Google Play Store’ da ‘Apple store’, manhajar zai ba da dama jama’a su san masu kokari da akasin haka.

   

Manhajoji
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Manhajoji
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Manhajoji
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.