ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Wasu Ɓarayin Mota 2 Da Ake Nema Ruwa A Jallo A Abuja

by Muhammad
2 years ago
Abuja

Rundunar ‘yansandan birnin tarayya Abuja ta ce jami’anta sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da satar mota a unguwar Mararaba da ke jihar Nasarawa.

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sandan birnin tarayya, SP Josephine Adeh, ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi a Abuja.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Sun Fasa Rumbun Ajiye Kayan Abinci A Abuja
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Farmaki Abuja Tare Da Sace Mutum 5

Ta ce an kama mutanen biyu ne a ranar 23 ga watan Afrilu da laifin satar motoci a babban birnin tarayya Abuja da kewaye.

ADVERTISEMENT

Adeh ta ce wadanda ake zargin suna cikin jerin sunayen da ‘yansandan ke nema ruwa a jallo tun watannin da suka gabata.

A cewarta, an kama wadanda ake zargin a wani otel da ke jihar Nasarawa a lokacin da suke karbar kudaden da suka cefanar da motar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

Ta ce an kwato motoci biyar da kayayyaki da dama daga hannun wadanda ake zargin.

Adeh ta ce kwamishinan ‘yan sanda mai kula da birnin tarayya Abuja, Benneth Igweh, ya umarci mazauna garin da su dauki duk matakan da suka dace don kare dukiyoyinsu.

Kwamishinan ya yi alkawarin tabbatar da samar da tsaron rayuka da dukiyoyi a birnin tarayya Abuja.

Igweh ya bukaci mazauna yankin da su sanya ido tare da yin amfani da layukan gaggawa na ‘yansanda wajen bayar da rahoton dukkan wash abubuwan da ba su dace ba ta wadannan lambobi 08032003913, 08028940883, 08061581938 da 07057337653.

Abuja
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft
Labarai

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft
Labarai

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kama Wani Fasinja Ɗauke Da Kwayar Tramadol 4,000 A Filin Jirgin Sama Na Legas

NDLEA Ta Kama Wani Fasinja Ɗauke Da Kwayar Tramadol 4,000 A Filin Jirgin Sama Na Legas

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.