• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim

‘Yan Arewa Mu Yi Wa Kanmu Karatun Ta-natsu, In Ji Shi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Siyasa
0
Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar Matasan Arewa da ke Kudancin Nijeriya ta yi gargaɗin cewa duk wani ɗan siyasa da ya shiga rigar Jagoran Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya lashe zaɓe kuma daga bisani ya kauce wa hanyar da Kwankwason ke bi, zai gani a ƙwaryar cin tuwonsa idan Allah ya kai mu zaɓen 2027.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin ne a wani taron manema labarai na musamman da ta kira a Kano domin faɗakar da ‘yan siyasa da kuma ‘yan arewa game da muhimmancin nuna kishin yankin musamman a yanzu da aka rantsar da sabuwar gwamnati a ƙasa baki ɗaya.
Da yake ƙarin haske ga wakilinmu bayan kammala taron, shugaban ƙungiyar, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya yi nuni da cewa, akwai ‘yan siyasa da dama da suka ci alfarmar jagoran na NNPP, Sanata Kwankwaso suka samu kujerun majalisa, “amma mun san ‘yan siyasar Nijeriya suna da wata ɗabi’a, za su shiga rigar mutum su samu abin da suke so, da zarar sun samu sai su kauce. To muna kira ga waɗanda suka shiga rigar ɗan kishin mutanen arewa da babu kamarsa wajen nuna wa al’ummarmu kishi, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, suka lashe zaɓe musamman a majalisun dokoki na ƙasa da na jihohi cewa kar su ci amana su kauce wa hanyarsa. Idan suka ƙi ji, to kowa ya sani, mu talakawa da muke da ƙuri’u a hannunmu za mu yi tsayin daka wajen ganin ba su koma ba, kowa zai gani a ƙwaryar cin tuwonsa.

  • Shugaban Nijeriya Na 16: Jan Aikin Da Ke Gaban Jagaban

“Abin da ya sa muke wannan kiran a kan Kwankwaso shi ne, duk cikin ‘yan siyasar da muke da su a arewa babu wanda yake nuna kishin al’umma a fili irin Kwankwaso. Mu da muke kudu, mun shaida irin yadda yake kai-komo a duk lokacin da aka ce ga wani abu ya samu wani ɗan arewa a can. Idan ba a manta ba, a zamanin da ɗan takarar shugaban ƙasa na LP, Peter Obi yake Gwamnan Anambara, ya bayar da umarni ga kowane ɗan arewa ya yi wata shaida da za a riƙa gane shi da ita. Ba tare da wani ɓata lokaci ba, shi ma Kwankwaso ya ce kowane Ibo da ke Kano ya yi uniform da za a riƙa gane su da shi.

“Haka nan lokacin da aka tsare mutanenmu a can. ƙungiyarmu musamman a Legas ita take ruwa da tsaki wurin fitar da mutanenmu da aka tsare daga gidan yari. Kuɗin da ake cin tarar mutanenmu daga kan dubu ɗaya har zuwa dubu ɗari (100,000) duk nakan yi ƙoƙarin biya ba tare da na saurari wani mai muƙami ko wata gwamnati ba. Aƙalla yanzu tsakanin kudu da arewa muna da mambobi sama da dubu takwas. Muna iya bakin ƙoƙari wajen ganin mun kare haƙƙin arewa, shi ya sa muke ƙara jaddada kira ga duk waɗanda suka kamata cewa mu yi wa kanmu karatun ta-natsu, idan Allah ya kai mu 2027 mu haɗa kai mu tabbatar da nasarar Sanata Kwankwaso a matsayinsa na ɗan kishin al’umma da ƙasa baki ɗaya.” In ji shi.

Wakazalika, Alhaji Ya’u Ibrahim Galadanci, ya buƙaci ‘yan siyasar da ke mayar da ‘ya`yan talakawa ‘yan shaye-shaye su sani Allah yana kallonsu kuma al’umma ba za ta ƙyale ba. “Sai dai su tura ‘ya’yansu zuwa ƙasashen Turai su yi karatu a can, amma sai su haɗa `ya’yan talakawa da kayan shaye-shaye don su riƙa amfani da su ana cin mutuncin masu mutunci. To, duk wannan ya kamata al’umma ta fito ta yi maganinsu ta hanyar ƙin zaɓarsu, idan aka yi haka za a samu sauƙi sosai ko kuma a magance lamarin.” Kamar yadda ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaKwankwasoSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Next Post

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Related

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

18 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

2 days ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Siyasa

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

3 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

4 days ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

4 days ago
Next Post
Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.