• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Kashe Naira Tiriyan 7, Har Yanzu Lantarkin Nijeriya Jiya-i-yau

Mun wallafa ran 27 ga Oktoba, 2023

by Sani Anwar
2 years ago
in Rahotonni
0
Duk Da Kashe Naira Tiriyan 7, Har Yanzu Lantarkin Nijeriya Jiya-i-yau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Duk da makudan kudaden da gwamnatin tarayya ta batar a harkar wutar lantarki, wanda ya kai kimanin naira tiriliyan bakwai, domin ganin wutar ta wadata a Nijeriya; hakarta ba ta cimma ruwa ba.

Har zuwa lokacin da gwamnatin ta yanke shawarar sayar da kamfanonin bangarorin samarwa da kuma rabon wutar lantarkin, tun a watan Nuwambar shekarar 2013; amma zuwa yanzu ba ta canza zani ba, domin kuwa matsalar dauke wutar lantarkin ta jima da zama ruwan dare ga ‘yan Nijeriya.

  • Gwamnan Katsina Ya Yi Wa Ma’aikatan Jihar Ƙarin ₦10,000 Kan Albashi, ‘Yan Fansho ₦5,000
  • INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

Binciken LEADERSHIP ya tabbatar da cewa, an samu katsewar wutar lantarki a fadin Nijeriya baki-daya har sau 223 daga shekarar 2010 zuwa wannan shekara da muke ciki.

A binciken, an tabbatar da katsewar wutar lantarkin a shekarar 2010, har sau kimanin 42, a shekarar 2011 sau 19, a 2012 sau 24, a 2013 sau 24, a 2014 sau 13, a 2015 sau 10, a 2016 sau 28, a 2017 sau 21, sai kuma sau 13 a 2018, sau 11 a 2019, sau 4 a 2020, sai kuma sau 4 a 2021. Daga shekarar 2022 zuwa yanzu, an samu wannan katsewar wutar lantarki; sau kimanin 10 a duk fadin Nijeriya.

Har ila yau, wannan katsewar wutar lantarki ta yi matukar kawo wa tattalin arzikin wannan kasa koma-baya, ta hanyar tafka asarar kimanin dalar Amurka miliyan 28, wanda ya yi daidai da kusan 2% na GDP dinmu na Nijeriya.

Daraktan Babban Bankin Duniya a Nijeriya, Shubham Chaudhuri, ya bayyana cewa; rashin tsayayyiyar wutar lantarki na matukar cutar da harkokin kasuwanci tare da samar ayyukan yi, wanda hakan zai iya tsamo a akalla mutane miliyan 100 daga kangin talauci.

Kamar yadda masana suka bayyana, katsewar wutar lantarki na afkuwa ne sakamakon dalilai da dama, wadanda suka hada da satar kayan wutar da lalata ta, matsalar rashin samar da gas, janyewar ruwa, yawan lodi da sauran makamantansu. Amma sun ce, gwamnatin na matukar kokari wajen ganin an gyara wannan matsala a halin yanzu.

Wani masanin harkar wutar lantarkin, Dakta Dayo Hassan ya bayyana cewa, tunda yanzu gwamnati ta dawo da mallakin hannunta tare da sanya ido a kan rabon wutar lantarkin, ta karkashin kamfanin rabon wutar lantarki ta kasa (TCN), ya zama wajibi gwamnatin ta sanya makudan kudade tare da inganta harkokin kimiyya (technology), domin magance matsalar sake katsewar wutar baki-daya.

Akwai rahotanni kimanin 108 da aka samu na lalata manyan tashoshin wutar lantarki daga watan Junairun 2022 zuwa watan Satumbar shekarar 2023 tare da sake lalata wasu tashoshin wutar guda tara a watan Mayun wannan shekara a Jihar Ogun.

Ire-iren wadannan matsaloli, sun faru kusan a yankuna daban- daban na fadin wannan kasa, ciki har da Benin, Abuja, Legas, Inugu da kuma Kano. Wasu daga cikin hare-haren da aka kai wa wadannan manya-manyan tashoshin wutar lantarki, na da alaka da hare-haren ‘yan kungiyar Boko Haram a Jihar Borno shekaru biyu da suka gabata, wanda hakan yake nuni da cewa; matsalar ba iya ta barayi masu sace-sace ba ne kadai, har da takidi na yi wa harkar zagon kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yankunan Raya Tattalin Arziki Na Sin Sun Samu Ci Gaban GDP A 2022

Next Post

Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

Related

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

21 hours ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

1 day ago
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

2 days ago
Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano
Rahotonni

Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

2 days ago
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

1 week ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

1 week ago
Next Post
Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.