ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Kashe Naira Tiriyan 7, Har Yanzu Lantarkin Nijeriya Jiya-i-yau

Mun wallafa ran 27 ga Oktoba, 2023

by Sani Anwar
3 years ago
Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Duk da makudan kudaden da gwamnatin tarayya ta batar a harkar wutar lantarki, wanda ya kai kimanin naira tiriliyan bakwai, domin ganin wutar ta wadata a Nijeriya; hakarta ba ta cimma ruwa ba.

Har zuwa lokacin da gwamnatin ta yanke shawarar sayar da kamfanonin bangarorin samarwa da kuma rabon wutar lantarkin, tun a watan Nuwambar shekarar 2013; amma zuwa yanzu ba ta canza zani ba, domin kuwa matsalar dauke wutar lantarkin ta jima da zama ruwan dare ga ‘yan Nijeriya.

  • Gwamnan Katsina Ya Yi Wa Ma’aikatan Jihar Ƙarin ₦10,000 Kan Albashi, ‘Yan Fansho ₦5,000
  • INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

Binciken LEADERSHIP ya tabbatar da cewa, an samu katsewar wutar lantarki a fadin Nijeriya baki-daya har sau 223 daga shekarar 2010 zuwa wannan shekara da muke ciki.

A binciken, an tabbatar da katsewar wutar lantarkin a shekarar 2010, har sau kimanin 42, a shekarar 2011 sau 19, a 2012 sau 24, a 2013 sau 24, a 2014 sau 13, a 2015 sau 10, a 2016 sau 28, a 2017 sau 21, sai kuma sau 13 a 2018, sau 11 a 2019, sau 4 a 2020, sai kuma sau 4 a 2021. Daga shekarar 2022 zuwa yanzu, an samu wannan katsewar wutar lantarki; sau kimanin 10 a duk fadin Nijeriya.

Har ila yau, wannan katsewar wutar lantarki ta yi matukar kawo wa tattalin arzikin wannan kasa koma-baya, ta hanyar tafka asarar kimanin dalar Amurka miliyan 28, wanda ya yi daidai da kusan 2% na GDP dinmu na Nijeriya.

Daraktan Babban Bankin Duniya a Nijeriya, Shubham Chaudhuri, ya bayyana cewa; rashin tsayayyiyar wutar lantarki na matukar cutar da harkokin kasuwanci tare da samar ayyukan yi, wanda hakan zai iya tsamo a akalla mutane miliyan 100 daga kangin talauci.

Kamar yadda masana suka bayyana, katsewar wutar lantarki na afkuwa ne sakamakon dalilai da dama, wadanda suka hada da satar kayan wutar da lalata ta, matsalar rashin samar da gas, janyewar ruwa, yawan lodi da sauran makamantansu. Amma sun ce, gwamnatin na matukar kokari wajen ganin an gyara wannan matsala a halin yanzu.

Wani masanin harkar wutar lantarkin, Dakta Dayo Hassan ya bayyana cewa, tunda yanzu gwamnati ta dawo da mallakin hannunta tare da sanya ido a kan rabon wutar lantarkin, ta karkashin kamfanin rabon wutar lantarki ta kasa (TCN), ya zama wajibi gwamnatin ta sanya makudan kudade tare da inganta harkokin kimiyya (technology), domin magance matsalar sake katsewar wutar baki-daya.

Akwai rahotanni kimanin 108 da aka samu na lalata manyan tashoshin wutar lantarki daga watan Junairun 2022 zuwa watan Satumbar shekarar 2023 tare da sake lalata wasu tashoshin wutar guda tara a watan Mayun wannan shekara a Jihar Ogun.

Ire-iren wadannan matsaloli, sun faru kusan a yankuna daban- daban na fadin wannan kasa, ciki har da Benin, Abuja, Legas, Inugu da kuma Kano. Wasu daga cikin hare-haren da aka kai wa wadannan manya-manyan tashoshin wutar lantarki, na da alaka da hare-haren ‘yan kungiyar Boko Haram a Jihar Borno shekaru biyu da suka gabata, wanda hakan yake nuni da cewa; matsalar ba iya ta barayi masu sace-sace ba ne kadai, har da takidi na yi wa harkar zagon kasa.

Lantarki
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.