ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Kashe Naira Tiriyan 7, Har Yanzu Lantarkin Nijeriya Jiya-i-yau

Mun wallafa ran 27 ga Oktoba, 2023

by Sani Anwar
2 years ago
Lantarki

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Duk da makudan kudaden da gwamnatin tarayya ta batar a harkar wutar lantarki, wanda ya kai kimanin naira tiriliyan bakwai, domin ganin wutar ta wadata a Nijeriya; hakarta ba ta cimma ruwa ba.

Har zuwa lokacin da gwamnatin ta yanke shawarar sayar da kamfanonin bangarorin samarwa da kuma rabon wutar lantarkin, tun a watan Nuwambar shekarar 2013; amma zuwa yanzu ba ta canza zani ba, domin kuwa matsalar dauke wutar lantarkin ta jima da zama ruwan dare ga ‘yan Nijeriya.

  • Gwamnan Katsina Ya Yi Wa Ma’aikatan Jihar Ƙarin ₦10,000 Kan Albashi, ‘Yan Fansho ₦5,000
  • INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

Binciken LEADERSHIP ya tabbatar da cewa, an samu katsewar wutar lantarki a fadin Nijeriya baki-daya har sau 223 daga shekarar 2010 zuwa wannan shekara da muke ciki.

A binciken, an tabbatar da katsewar wutar lantarkin a shekarar 2010, har sau kimanin 42, a shekarar 2011 sau 19, a 2012 sau 24, a 2013 sau 24, a 2014 sau 13, a 2015 sau 10, a 2016 sau 28, a 2017 sau 21, sai kuma sau 13 a 2018, sau 11 a 2019, sau 4 a 2020, sai kuma sau 4 a 2021. Daga shekarar 2022 zuwa yanzu, an samu wannan katsewar wutar lantarki; sau kimanin 10 a duk fadin Nijeriya.

Har ila yau, wannan katsewar wutar lantarki ta yi matukar kawo wa tattalin arzikin wannan kasa koma-baya, ta hanyar tafka asarar kimanin dalar Amurka miliyan 28, wanda ya yi daidai da kusan 2% na GDP dinmu na Nijeriya.

Daraktan Babban Bankin Duniya a Nijeriya, Shubham Chaudhuri, ya bayyana cewa; rashin tsayayyiyar wutar lantarki na matukar cutar da harkokin kasuwanci tare da samar ayyukan yi, wanda hakan zai iya tsamo a akalla mutane miliyan 100 daga kangin talauci.

Kamar yadda masana suka bayyana, katsewar wutar lantarki na afkuwa ne sakamakon dalilai da dama, wadanda suka hada da satar kayan wutar da lalata ta, matsalar rashin samar da gas, janyewar ruwa, yawan lodi da sauran makamantansu. Amma sun ce, gwamnatin na matukar kokari wajen ganin an gyara wannan matsala a halin yanzu.

Wani masanin harkar wutar lantarkin, Dakta Dayo Hassan ya bayyana cewa, tunda yanzu gwamnati ta dawo da mallakin hannunta tare da sanya ido a kan rabon wutar lantarkin, ta karkashin kamfanin rabon wutar lantarki ta kasa (TCN), ya zama wajibi gwamnatin ta sanya makudan kudade tare da inganta harkokin kimiyya (technology), domin magance matsalar sake katsewar wutar baki-daya.

Akwai rahotanni kimanin 108 da aka samu na lalata manyan tashoshin wutar lantarki daga watan Junairun 2022 zuwa watan Satumbar shekarar 2023 tare da sake lalata wasu tashoshin wutar guda tara a watan Mayun wannan shekara a Jihar Ogun.

Ire-iren wadannan matsaloli, sun faru kusan a yankuna daban- daban na fadin wannan kasa, ciki har da Benin, Abuja, Legas, Inugu da kuma Kano. Wasu daga cikin hare-haren da aka kai wa wadannan manya-manyan tashoshin wutar lantarki, na da alaka da hare-haren ‘yan kungiyar Boko Haram a Jihar Borno shekaru biyu da suka gabata, wanda hakan yake nuni da cewa; matsalar ba iya ta barayi masu sace-sace ba ne kadai, har da takidi na yi wa harkar zagon kasa.

Lantarki
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.