ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Kashe Naira Tiriyan 7, Har Yanzu Lantarkin Nijeriya Jiya-i-yau

Mun wallafa ran 27 ga Oktoba, 2023

by Sani Anwar
2 years ago
Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Duk da makudan kudaden da gwamnatin tarayya ta batar a harkar wutar lantarki, wanda ya kai kimanin naira tiriliyan bakwai, domin ganin wutar ta wadata a Nijeriya; hakarta ba ta cimma ruwa ba.

Har zuwa lokacin da gwamnatin ta yanke shawarar sayar da kamfanonin bangarorin samarwa da kuma rabon wutar lantarkin, tun a watan Nuwambar shekarar 2013; amma zuwa yanzu ba ta canza zani ba, domin kuwa matsalar dauke wutar lantarkin ta jima da zama ruwan dare ga ‘yan Nijeriya.

  • Gwamnan Katsina Ya Yi Wa Ma’aikatan Jihar Ƙarin ₦10,000 Kan Albashi, ‘Yan Fansho ₦5,000
  • INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

Binciken LEADERSHIP ya tabbatar da cewa, an samu katsewar wutar lantarki a fadin Nijeriya baki-daya har sau 223 daga shekarar 2010 zuwa wannan shekara da muke ciki.

A binciken, an tabbatar da katsewar wutar lantarkin a shekarar 2010, har sau kimanin 42, a shekarar 2011 sau 19, a 2012 sau 24, a 2013 sau 24, a 2014 sau 13, a 2015 sau 10, a 2016 sau 28, a 2017 sau 21, sai kuma sau 13 a 2018, sau 11 a 2019, sau 4 a 2020, sai kuma sau 4 a 2021. Daga shekarar 2022 zuwa yanzu, an samu wannan katsewar wutar lantarki; sau kimanin 10 a duk fadin Nijeriya.

Har ila yau, wannan katsewar wutar lantarki ta yi matukar kawo wa tattalin arzikin wannan kasa koma-baya, ta hanyar tafka asarar kimanin dalar Amurka miliyan 28, wanda ya yi daidai da kusan 2% na GDP dinmu na Nijeriya.

Daraktan Babban Bankin Duniya a Nijeriya, Shubham Chaudhuri, ya bayyana cewa; rashin tsayayyiyar wutar lantarki na matukar cutar da harkokin kasuwanci tare da samar ayyukan yi, wanda hakan zai iya tsamo a akalla mutane miliyan 100 daga kangin talauci.

Kamar yadda masana suka bayyana, katsewar wutar lantarki na afkuwa ne sakamakon dalilai da dama, wadanda suka hada da satar kayan wutar da lalata ta, matsalar rashin samar da gas, janyewar ruwa, yawan lodi da sauran makamantansu. Amma sun ce, gwamnatin na matukar kokari wajen ganin an gyara wannan matsala a halin yanzu.

Wani masanin harkar wutar lantarkin, Dakta Dayo Hassan ya bayyana cewa, tunda yanzu gwamnati ta dawo da mallakin hannunta tare da sanya ido a kan rabon wutar lantarkin, ta karkashin kamfanin rabon wutar lantarki ta kasa (TCN), ya zama wajibi gwamnatin ta sanya makudan kudade tare da inganta harkokin kimiyya (technology), domin magance matsalar sake katsewar wutar baki-daya.

Akwai rahotanni kimanin 108 da aka samu na lalata manyan tashoshin wutar lantarki daga watan Junairun 2022 zuwa watan Satumbar shekarar 2023 tare da sake lalata wasu tashoshin wutar guda tara a watan Mayun wannan shekara a Jihar Ogun.

Ire-iren wadannan matsaloli, sun faru kusan a yankuna daban- daban na fadin wannan kasa, ciki har da Benin, Abuja, Legas, Inugu da kuma Kano. Wasu daga cikin hare-haren da aka kai wa wadannan manya-manyan tashoshin wutar lantarki, na da alaka da hare-haren ‘yan kungiyar Boko Haram a Jihar Borno shekaru biyu da suka gabata, wanda hakan yake nuni da cewa; matsalar ba iya ta barayi masu sace-sace ba ne kadai, har da takidi na yi wa harkar zagon kasa.

Lantarki
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Lantarki
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Lantarki
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

Cikakken Dalilin Shirin Ficewar ‘Shoprite’ Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.