• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Durkushewar Masana’antun Auduga Na Ci Gaba Da Ci Wa Al’umma Tuwo A Kwarya

by Bello Hamza
1 year ago
in Rahotonni
0
Durkushewar Masana’antun Auduga Na Ci Gaba Da Ci Wa Al’umma Tuwo A Kwarya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ci gaba da nuna damuwa a kan yadda masaku da masana’antun sarrafa auduga suka durkushe shekara da shekaru a fadin kasar nan, da kuma yadda noman auduga da ya kasance wata kafa ta samun arziki a arewa ya zama tarihi a yanzu.

A shekarun baya masana’antun sarrafa auduga (masaku) sun bayar da gudummawa sosai ga bunkasar tattalin arzikin kasa.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Yawan Motocin Da Sin Ta Sayar Ya Kai Miliyan 6.72 A Rubu’in Farkon Bana

Noman auduga ya kasance wata kafar samun kudaden shiga ga manoma da ‘yan kasuwa da kuma kayan aiki ga masana’antu da masakun da muke da su a fadin Nijeriya haka kuma yana samar wa da matasa da dama aikin yi, amma kuma abin takaici a halin yanzu shi ne yadda wadannan masakun suka durkushe abin da ya yi sanadiyyar rasa ayyukan yi ga al’umma masu yawa.

Dalilai da dama suka yi sandiyyar durkushewar da aka samu wadanda suka hada da rashin ingantaccen tsare-tsare daga gwamnati, dumamar yanayi, rashin kayan aiki na zamani da kuma yadda ake shigo da auduga mai saukin kudi daga kasashen waje wanda wasu ‘yan kasuwa suka shiga yi.

Dubban manoman da suka dogara ga harkokin da suka shafi noma da sarrafa audugan sun shiga tasku haka kuma tattalin arzikin yanki ya samu koma-baya.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Binciken da LEADERSHIP Hausa ta yi, ya nuna cewa kananan kamfanonin sarrafa auduga da ke garuruwan Kaduna, Kano, Katsina, Sakkwato da Zamfara duk sun durkushe.

Haka kuma manoma a wadannan jihohin da suke samar wa da wadannan masana’antun kayan aiki duk sun yi watsi da noman saboda rashin masu hulda da su.

Misali a Jihar Kano da ake da manoman auduga fiye da 26,000 a shekarar 2019 yanzu sun ragu zuwa 24,500 a shekarar 2020. Yawancinsu sun amfana da shirin bashi na ‘Anchor Borrowers’’ da CBN ya bayar.

A tattaunawarsa da LEADERSHIP Hausa, shugaban kungiyar masu noman auduga ta Nijeriya, reshen jihar Kano, Ibrahim Abdulhamid ya bayyana cewa, “A shekarar 2019, lokacin da gwamnmati ta bayar da tallafin aikin noma, an samu manoma 26,000 amma a shekarar 2020, adadin wadanda suka shiga shirin ya koma 24,500 amma a halin yanzu da wuya ka samu manoma 2,000 da ke harkar noman auduga a Jihar Kano. Binciken da muka yi a wasu jihohin ya nuna lamarin kusan duk daya ne.

Saboda a halin yanzu Nijeriya ta sauko a matsayinta na shugaba a Afrika ta masu noman auduga.

Wani rahoto da aka wallafa a kafar ‘mordorintelligence.com/industry-reports/africa-cotton-market’ ya nuna cewa, yawancin kanana manoma ne ke a kan gaba wajen noman auduga, duk da ana samun wasu manyan gonaki, hakan na faruwa ne saboda yawanci ana noma auduga ne a matsayin hanyar samun kudin shiga, kuma a halin yanzu babu kasuwar.

Wani abin lura kuma shi ne kasashe kalilan ne a Afrika ke amfani da ingantattun irin auduga da aka alkinta, sun kuma hada da kasashen Afrika ta Kudu, Sudan, Barkina Faso a nan ne kuma ake samun manoman da suke amfani da irin audugan da aka alkinta wadanda ke bayar da yabanya mai yawa.

Bincike ya nuna cewa, kasashen Mali, Burkina Faso, da Kwadebuwa ke a kan gaba wajen samar da auduga a Afrika inda suke bayar da kashi 50 na audugan da ake da shi a yankin Afrika gaba daya.

Kasashe da suka fi sayen auduga daga Afrika sun hada da Bangladesh, Bietnam,  da Malaysia. An fi samun samun auduga ne a yanayi mai dumi da kasa mai damshi shi ya sa yankin Saharan Afrika ya kasance wurin da aka fi noma auduga a duniya gaba daya.

A jawabinsa, shugaban hukumar kula da harkar gona ta Jihar Kano, Gambo Isa Garko, ya tabbata da raguwar harkar noman auduga a jihar inda ya alakanta hakan a kan rashin ingantattun irin shukawa da kuma farmakin kwari.

Ya ce, audugan da aka fi nomawa a lokacin damuna ya samu bunkasa ne a jihar a tsakanin shekarar 2019 zuwa 2020 lokacin da gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta kaddamar da shirin ‘anchor borrowers’ don tallafa wa manoman auduga a kasar nan.

A cewarsa a lokacin da manoma suka samu tattalin an samu karuwa noman auduga amma a lokacin da aka dakatar da tallafin noman audugan ya tsaya cik.

“A lokacin an tallafa wa kamfanoni domin su farfado da ayyukansu, amma daga karshe kamfanonin sun kasa ci gaba da aiki saboda ba zai yiwu su sayar da kayan su a farashin da ya dace ba saboda yadda suke samun kayan tun da farko a kan haka suma manona suka dakatar da noman audugan saboda rashin masu saya, musamman kuma rashin ingantaccen farashi.

“A kan haka yawacin kamfanonin da ke da alaka da harkar masaku suka daina aiki abin ya kai ga kamfanoni masu samar da sinadarai duk suka durkushe gaba daya.

“Ya ce, saboda babu isasun manoman da za su samar wa kamfanonin auduga kayan aiki, wadannan ne matsalolin da suka hadu suka yi wa harkar katutu.

Lamarin duk daya ne a ta bakin shugaban kungiyar masu noma auduga na (NACOTAN), Ibrahim Abdulhamid, ya kuma kara da cewa, matsalolin da harkar noman auduga ya fuskanta har aka samu ragowa da kashi 70 sun hada da rashin cikakken sanya kudi daga gwamnati da rashin malaman gona masu bayar da shawarwari da mastalar tsaron da ake fuskanta a wasu sassan yankin arewa. Ya ce yankuna irinsu kananan hukumomin Karaye da Gwarzo da suke a tsakanin iyakokin Jihar Katsina suna fuskantar matsalolin ‘yan bindiga wanda hakan ya hana su shiga harkar noman samar da auduga.

Darakta a ma’aikatar masana’antu da zuba jari na jihar Kano, Mamoud Bala, ya nuna takaicinsa a kan yadda masana’antun masaku da dama a Jihar Kano suka durkushe gaba daya. Ya ce, a baya wurare irinsu Bompai, Sharada, da Chalawa sun kasance fagen da manyan masaku suke harkokinsu amma a halin yanzu duk sun durkushe.

Ya kuma dora alhakin wannan ne a kan rashin isasshen wutar lantarki, fasakwauri da shiga da kayayyaki da kasar Chana da wasu kasaashe duniya.

Masakun da aka farfado da su a Katsina ba sa aiki yadda ya kamata

A kokarin farfado da noma auduga domin samun abubuwan da masana’antu za su yi amfani da su, gwamnatin Jihar Katsina ta farfado na noman rani a fadin jihar gaba daya don samar da auduga.

Wannan na daga cikin tsare tsaren gwamnan jihar Dikko Umaru Radda na shigo da aikin gona na zamani don samar da kudaden shuiga da bunkasa tattalin arzikin jihar.

Shugaban kungiyar manoma ta ‘All Farmers’ Association of Nigeria (AFAN), Umar Ya’u Gwajo-Gwajo, wanda ya sanar da haka a tattunamawarsu da wakilinmu, ya kara cewa, gamnatin jihar ta fito da wasu shirye-shirye na samawar wa da manoma kayan aiki na zamani ta hannun kungiyar don kara bunkasa harkar noma a fadin jihar.

Ya ce, an shirya amfani da manoman auduga ne don amfanar manoman da gwanmnati da kuma bukatar farfado da masana’antun da muke da su a fadin jihar, a kan haka gwamnati ta dauki ma’aikatan gona don cimma nasarar wannan shirin.

Manoman Jihar Kwara Sun Nemi Tallafin Gwsmanati A Kan Noman Auduga

A halin yanzu kuma manoman auduga a Jihar Kwara sun nemi gamnatin jihar ta tallafa musu da kayan aki kamar takin zamani don inganta aikin su.

Manoman audugan da aka fi samu a yankuna kananan hukumonin Kwara North da Kaiama sun mika wannan bukatar ne a tattaunawarsu da LEADERSHIP Hausa a babban birnin jihar Ilorin.

Sun bayyana wannan bukatar ne a ta bakin shugaban kungiyar manoman Jihar Kwara, Hon. Umar Mahmud Aboki, wanda kuma yana cikin manya-manyan manoman auduga na Jihar Kwara.

Ya kara da cewa, babu kamfanoni masu sarrafa auduga a jihar amma wasu mabukata daga wasu jihohin arewa suke shigowa don sayen audugan da aka noma.”

LEADERSHIP Hausa ta lura da cewa, masaka daya tilo da ke jihar Kwara ta daina aiki ne tun zamanin mulkin sojoji a Nijeriya.

Haka kuma mai ba gwamnan shawara na musamman, a kan harkokin yada labarai, Alhaji Bashir Adigun ya ce, gwamnati na taimaka wa dukkan manoma a jihar ciki har da manoman auduga da taki da kuma ingantaccen iri don inganta harkar noman su.

Labarin kusan daya yake a jihohin Sakwkato, lamarin noman auduga ya ja da baya sosai a ‘yan shekarun nan. A ta bakin Sani Tangaza wani dan shekara 54, ya bayyana yadda ya samu mahaifinsa marigayi Alhaji Sani Abdullahi, a harkar saye da sayar da auduga, inda yake kasuwancin auduga daga nan zuwa garin Futunwa ta Jihar Katsina amma a halin yanzu lamarin ya zama labari.

“A yau dai muna da filayen noma amma harkar noma ya tsaya tun daga lokacin da masana’antun masaku suka durkushe.

Da yawa daga cikin wadanda suka tattunawa da jaridar EADERSHIP sun nemi gwamnatin jihoji 19 na arewacin kasar nan su hada hannu wajen farfado da masana’antu da harkar noman auduga a kasar nan ta hanyar samarwa da manoman tallafi na musamman na kayan aiki na zamani.

Sun ce, farfado da harkar noman auduga a kasar nan za ta taimaka wajen samar da aikin yi ga al’umma sannan za ta taimaka wajen samar da aikin yi ga dimbin matasanmu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Barka Da Sallah: Shugabanni Sun Yi Kiran Amfani Da Darussan Ramadan

Next Post

Yadda Na Hada Gidan Rediyon Da Ake Ji A Jihohi Takwas –Injiniya Yakubu

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Auduga
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Yadda Na Hada Gidan Rediyon Da Ake Ji A Jihohi Takwas –Injiniya Yakubu

Yadda Na Hada Gidan Rediyon Da Ake Ji A Jihohi Takwas –Injiniya Yakubu

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.