Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

FRSC Ta Gurfanar Da Masu Laifuka 157 Gaban Kuliya A Bauchi

by Muhammad
January 11, 2021
in LABARAI
2 min read
Hukumar FRSC
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya,

Shiyya ta goma sha biyu, ta hukumar kiyaye hatsaruka kan hanyoyin kasar nan (FRSC), ta bayyana cewar, kotun tafi da gidan-ka ta hukumar a rukunin zaman ta na farko a garuruwan Bauchi, Toro, Azare, da Bara ta kama masu laifi guda dari da hamsin da bakwai (157) wadanda aka gurfanar da su a gaban kuliya.

samndaads

Wannan bayani ya na dauke ne cikin wata sanarwa da hukumar ta kiyaye hatsaruka, wanda jami’in ta ACM Rotimi T. Adeleye ya sanya hannu kuma aka rarraba wa manema labarai a garin Bauchi shekaran jiya.

A cewar sanarwar, masu laifuka 145 an yi masu hukunce-hukunce kan laifuka daban-daban dangane da sufuri kan hanyoyi, yayin da kotu ta sallami guda goma sha-biyu daga cikin su.

“Daga gefe guda kuma, hukumar ta lura da wasu majibantan hanyoyi da suke aikata ba daidai ba. Wadannan kamfanoni ko hukumomi masu ayyukan safara, hukumar za ta zayyana masu ka’idojin safara kan hanyoyin kasar nan. Za a sanar da ofisoshin wadannan kamfanoni ko hukumomi kamar yadda ya dace.”

Sanarwar ta cigaba da cewa, “Rashin sanya na’urar gwajin tafiya akan hanya, dibar kaya fiye da kima da matsanancin gudu akan hanya su ne mafi munin laifuka da masu safara akan hanyoyi ke aikatawa. Wannan hukuma ta na kira ga masu tuki akan hanyoyi da su rika kiyaye dokokin safara domin kiyaye lafiyar su, hadi da masu amfani da hanyoyi.

“Ya na kuma da muhimmanci matuka da ka’idojin kariya daga cutar sarke numfashi (Korona) kamar amfani da Amawali, Kula da Tazara Tsakanin mutum-da-mutum, da wanke hannaye yayin tafiye-tafiye”.

Hukumar ta kiyaye hatsaruka ta yaba matuka-gaya yadda matuka ababen hawa suke kiyaye dokokin safara, musamman a lokutan shagulgula, hadi da hadin kai da masu safara suke baiwa hukumar ta kiyaye hatsaruka a yayin gudanar da ayyukan ta a shekara da ta gabata, husasan la’akari da zaman kotun tafi-da-gidanka a wannan shiyya.

Sanarwar ta hukumar, ta shawarci ‘yan-kasuwa, musamman masu tsuguni-tashi da su kauracewa gefen hanyoyi domin baiwa hanyoyin hakkokin su, musamman a lokutan shagulgulan al’adu ko addini domin kiyaye faruwar hatsaruka, kamar yadda hukumar ta ke jaddada jajircewar ta kan fadakar da al’umma.

SendShareTweetShare
Previous Post

CAN Ta Jinjina Wa Gwamna Inuwa Bisa Kyautata Zaman Lafiya A Gombe

Next Post

Hukumar NDE Ta Kaddamar Da Shirin Koya Wa Matasa Sana’a A Zamfara

RelatedPosts

NIS Da NAPTIP Sun Sake Shan Damarar Yaki Da Safarar Dan Adam

NIS Da NAPTIP Sun Sake Shan Damarar Yaki Da Safarar Dan Adam

by Yahuzajere
4 hours ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) da...

Sabuwar Cuta Ta Kashe Mutum Hudu A Sokoto

Sabuwar Cuta Ta Kashe Mutum Hudu A Sokoto

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Gwamna jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal Ya sanar da Mutuwar...

Sakatariyar

Sakatariyar Karamar Hukumar Da Ake Wata Guda Ba A Shige Ta Ba A Kano

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kananan Hukumomi ne ke zaman gimshikai...

Next Post
NDE

Hukumar NDE Ta Kaddamar Da Shirin Koya Wa Matasa Sana'a A Zamfara

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version