ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Da Shugabannin APC Na Kano Sun Amince Da Tinubu A 2027

by Abubakar Sulaiman
4 weeks ago
Ganduje

Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, tare da manyan shugabannin jam’iyyar APC daga ƙananan hukumomi 44 na jihar, sun amince da sake tsayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar a zaben 2027.

Ganduje ya sanar da hakan ne bayan jerin tarukan shawarwari da ya gudanar da shugabannin jam’iyyar a gidansa da ke Kano, yana mai cewa tattaunawar na da nufin ƙarfafa haɗin kai da tsare-tsaren jam’iyya kafin babban zaɓe mai zuwa.

  • Jami’an APC 3 A Jihar Zamfara Da Aka Dakatar Sun Maka Jam’iyyar A Kotu
  • Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

A jawabinsa, Ganduje ya ce burinsu shi ne tabbatar da cikakken zaman lafiya da daidaito a jam’iyyar daga mataki na ƙasa zuwa na sama, tare da nuna goyon baya ga gwamnatin tarayya ƙarƙashin Shugaba Tinubu. Ya umarci shugabannin jam’iyya a matakan ƙananan hukumomi da mazaɓu da su tabbatar da buɗe ofisoshin APC a kowane yanki domin karɓar sabbin mambobi.

ADVERTISEMENT

Ganduje ya kuma bayyana cewa za a ƙara ƙaimi a aikin rajistar mambobin jam’iyya ta hanyar amfani da tsarin zamani na diigital. Don haka, kowace ƙaramar hukuma za ta tura ma’aikatan ICT guda uku da aka horar domin jagorantar aikin, tare da niyyar faɗaɗa yawan mambobin jam’iyyar kafin zaɓen 2027. Haka kuma ya ja hankalin mambobi su bi ƙa’idojin INEC ta hanyar tabbatar da cewa dukkan masu shekaru 18 da haihuwa sun yi rijistar zabe bisa tsarin da ake gudanarwa a fadin ƙasa.

Jiga-jigan jam’iyyar da suka halarci taron sun haɗa da tsohon Gwamnan Kano Kabiru Ibrahim Gaya, da ɗan majalisar wakilai Alhassan Ado Doguwa, da ɗan takarar gwamna na 2023 Nasiru Yusuf Gawuna da mataimakinsa Murtala Sule Garo, Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas da sauran fitattun shugabannin jam’iyyar a Kano.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Sai dai ba a hango mataimakin shugaban majalisar dattawa ba Bari Jibrin da ƙaramin ministan gidaje Yusuf Ata ba, wanda wannan ta ƙara haska cewa akwai ɓarakar da zata iya raba jam’iyyar gida biyu a zaɓen 2027.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Li Qiang Ya Halarci Zama Na Biyu Da Na Uku Na Taron Kolin G20 Karo Na 20

Li Qiang Ya Halarci Zama Na Biyu Da Na Uku Na Taron Kolin G20 Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.