ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Da Shugabannin APC Na Kano Sun Amince Da Tinubu A 2027

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Ganduje

Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, tare da manyan shugabannin jam’iyyar APC daga ƙananan hukumomi 44 na jihar, sun amince da sake tsayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar a zaben 2027.

Ganduje ya sanar da hakan ne bayan jerin tarukan shawarwari da ya gudanar da shugabannin jam’iyyar a gidansa da ke Kano, yana mai cewa tattaunawar na da nufin ƙarfafa haɗin kai da tsare-tsaren jam’iyya kafin babban zaɓe mai zuwa.

  • Jami’an APC 3 A Jihar Zamfara Da Aka Dakatar Sun Maka Jam’iyyar A Kotu
  • Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

A jawabinsa, Ganduje ya ce burinsu shi ne tabbatar da cikakken zaman lafiya da daidaito a jam’iyyar daga mataki na ƙasa zuwa na sama, tare da nuna goyon baya ga gwamnatin tarayya ƙarƙashin Shugaba Tinubu. Ya umarci shugabannin jam’iyya a matakan ƙananan hukumomi da mazaɓu da su tabbatar da buɗe ofisoshin APC a kowane yanki domin karɓar sabbin mambobi.

ADVERTISEMENT

Ganduje ya kuma bayyana cewa za a ƙara ƙaimi a aikin rajistar mambobin jam’iyya ta hanyar amfani da tsarin zamani na diigital. Don haka, kowace ƙaramar hukuma za ta tura ma’aikatan ICT guda uku da aka horar domin jagorantar aikin, tare da niyyar faɗaɗa yawan mambobin jam’iyyar kafin zaɓen 2027. Haka kuma ya ja hankalin mambobi su bi ƙa’idojin INEC ta hanyar tabbatar da cewa dukkan masu shekaru 18 da haihuwa sun yi rijistar zabe bisa tsarin da ake gudanarwa a fadin ƙasa.

Jiga-jigan jam’iyyar da suka halarci taron sun haɗa da tsohon Gwamnan Kano Kabiru Ibrahim Gaya, da ɗan majalisar wakilai Alhassan Ado Doguwa, da ɗan takarar gwamna na 2023 Nasiru Yusuf Gawuna da mataimakinsa Murtala Sule Garo, Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas da sauran fitattun shugabannin jam’iyyar a Kano.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Sai dai ba a hango mataimakin shugaban majalisar dattawa ba Bari Jibrin da ƙaramin ministan gidaje Yusuf Ata ba, wanda wannan ta ƙara haska cewa akwai ɓarakar da zata iya raba jam’iyyar gida biyu a zaɓen 2027.

Ganduje
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Li Qiang Ya Halarci Zama Na Biyu Da Na Uku Na Taron Kolin G20 Karo Na 20

Li Qiang Ya Halarci Zama Na Biyu Da Na Uku Na Taron Kolin G20 Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.