ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Da Shugabannin APC Na Kano Sun Amince Da Tinubu A 2027

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Ganduje

Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, tare da manyan shugabannin jam’iyyar APC daga ƙananan hukumomi 44 na jihar, sun amince da sake tsayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar a zaben 2027.

Ganduje ya sanar da hakan ne bayan jerin tarukan shawarwari da ya gudanar da shugabannin jam’iyyar a gidansa da ke Kano, yana mai cewa tattaunawar na da nufin ƙarfafa haɗin kai da tsare-tsaren jam’iyya kafin babban zaɓe mai zuwa.

  • Jami’an APC 3 A Jihar Zamfara Da Aka Dakatar Sun Maka Jam’iyyar A Kotu
  • Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

A jawabinsa, Ganduje ya ce burinsu shi ne tabbatar da cikakken zaman lafiya da daidaito a jam’iyyar daga mataki na ƙasa zuwa na sama, tare da nuna goyon baya ga gwamnatin tarayya ƙarƙashin Shugaba Tinubu. Ya umarci shugabannin jam’iyya a matakan ƙananan hukumomi da mazaɓu da su tabbatar da buɗe ofisoshin APC a kowane yanki domin karɓar sabbin mambobi.

ADVERTISEMENT

Ganduje ya kuma bayyana cewa za a ƙara ƙaimi a aikin rajistar mambobin jam’iyya ta hanyar amfani da tsarin zamani na diigital. Don haka, kowace ƙaramar hukuma za ta tura ma’aikatan ICT guda uku da aka horar domin jagorantar aikin, tare da niyyar faɗaɗa yawan mambobin jam’iyyar kafin zaɓen 2027. Haka kuma ya ja hankalin mambobi su bi ƙa’idojin INEC ta hanyar tabbatar da cewa dukkan masu shekaru 18 da haihuwa sun yi rijistar zabe bisa tsarin da ake gudanarwa a fadin ƙasa.

Jiga-jigan jam’iyyar da suka halarci taron sun haɗa da tsohon Gwamnan Kano Kabiru Ibrahim Gaya, da ɗan majalisar wakilai Alhassan Ado Doguwa, da ɗan takarar gwamna na 2023 Nasiru Yusuf Gawuna da mataimakinsa Murtala Sule Garo, Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas da sauran fitattun shugabannin jam’iyyar a Kano.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Sai dai ba a hango mataimakin shugaban majalisar dattawa ba Bari Jibrin da ƙaramin ministan gidaje Yusuf Ata ba, wanda wannan ta ƙara haska cewa akwai ɓarakar da zata iya raba jam’iyyar gida biyu a zaɓen 2027.

Ganduje
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote
  • Abubakar Sulaiman
    Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Li Qiang Ya Halarci Zama Na Biyu Da Na Uku Na Taron Kolin G20 Karo Na 20

Li Qiang Ya Halarci Zama Na Biyu Da Na Uku Na Taron Kolin G20 Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.