Daga Abba Ibrahim Wada
Dan wasan Najeriya dake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Leicester City, Kelechi Iheanacho, yayi bajinta a ranar Lahadi, bayan jefa kwallaye uku shi kadai a ragar kungiyar Sheffield United, a wasan da suka lallasa ta da ci 5-0.
Nasarar ta Leicester City, ta bata damar darewa mataki na uku da maki 56, bayan da daga bisani Manchester United ta sake komawa kan matsayi na biyun a gasar ta Firimiya bayan doke West Ham da 1-0 a ranar Lahadi.
Ita kuwa kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta kara tazarar makin dake tsakaninta da mabiyanta a Firimiyar bayan lallasa kungiyar Fulham da ci 3-0 a ranar Asabar, nasarar da ta bata jumilar maki 71, maki 14 tsakaninta Manchester United dake biye da ita a matsayi na 2 da kwantan wasa daya.
dan wasan gaban kungiyar, Gabriel Jesus, da Sergio Aguero da kuma John Stones ne suka ciwa Manchester City kwallayen da suka kara kusantar da ita ga samun nasarar lashe kofin gasar Firimiya na farko cikin shekaru 4.
Ita kuwa kungiyar Arsenal ta samu nasara kan Tottenham da kwallaye 2-1 ne ta hannun ‘yan wasanta Martin Odegaard da kuma Aledander Lacazette duk da cewa kungiyar Tottenham ce ta soma jefa kwallo a ragar Arsenal ta hannun dan wasan ta Lamela, kafin daga bisani reshe ya juye da mujiya kuma sakamakon ya nuna a halin yanzu Arsenal na matsayi na 10 da maki 41, yayin da Tottenham ke matsayi na 7 da maki 45.