• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya An Noma Masara Da Tsadar Gaske A Bana – Shugaban Manoma

by Abubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
in Noma Da Kiwo
0
tela maize
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bukaci matakan gwamnati uku na kasar nan, su mayar da hankali kan bunkasa noman rani.

 

Shugaban Kungiyar Manoman Masara, don samun riba na yankin Arewa Maso Gabas; Alhaji Adamu Muhammad Makarfi ne ya yi wannan kira.

  • Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan
  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a Kaduna, Makarfi ya yi nuni da cewa; ya zama wajibi a samar da kyakkyawan tsari, idan kuma ba haka ba; ba mu san irin abin da zai faru a wannan kasa nan gaba ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Da yake yin tsokaci kan tsarin da gwamnatin tarayya ta fito da shi na dakile ‘yan kasuwar kasar waje zuwa gonakin manoma, don saye amfanin gonar da suka noma kai tsaye; ya ce; wannan tsari abin a yaba ne.

 

Sai dai, Makarfin ya sanar da cewa; gwamnatin ta makara wajen daukar wannan mataki, domin tuntuni ya kamata a ce an yi wannan tsari.

 

Har ila yau, a kan kakar noman bana kuwa; Makarfin ya bayyana yadda suka sayi takin zamani da tsada a noman Masarar bana da suka yi.

 

A cewar tasa, tsadar takin yasa; musamman kanannan manoman Masara Jihar Kaduna, ba su samu damar iya sayen takin ba; ballantana su noma ta.

 

Ya ce, a bana farashinsa ya ninka; hatta magungunan feshi na kwari ko na kashe Ciyawa da kudin kwadago, dukkaninsu kudaden sun karu.

 

Ya ci gaba da cewa, haka nan ambaliyar ruwan sama da aka samu a wasu jihohin, kamar Borno, Jigawa da sauransu; hakan ya sake jawo wa wasu manoman yin asara.

 

Ya kara da cewa, “A matsayina na manomi, bukatarmu ba a sayar da amfanin gona da tsada ba, amma duk da haka; ba za mu so a ce manoma sun yi asara ba, domin asarar manoma; asara ce ga kasa baki-daya”, in ji shi.

 

Kazalika, ya yi nuni da cewa; duk inda aka ce manomi ya yi noma ya samu faduwa, babban abin da ake jin tsaro; musamman manyan manoma da yawancinsu ke yin noma, don riba; idan suka fadi to fa akwai matsala, domin akasarinsu na ciwo bashi ne a bankuuna; domin yin noman da kuma kudin ruwan da ake dora musu, asarar za ta yi musu yawa.

 

Shugaban ya ci gaba da cewa, idan manyan manoma ba su yi noma a kasar nan ba, za a samu karancin abinci; hakan ne yasa za ka ga ana yin kira a je a sayo abinci daga kasashen ketare, wanda kuma idan aka yi hakan; ko shakka babu Nijeriya za ta iya yin asara mai yawa, wanda ka iya durkusar da tattalin arzikinta.

 

A karshe, ya bayyana cewa; idan har za a sayo Masara a kasar waje ba tare da an noma a cikin gida ba, akalla za a iya yin asarar kimanin Naira tirilyan goma; inda ya yi nuni da cewa, idan ba a bai wa manoman kasar nan taimakon da ya dace ba; karamar matsala ce za ta iya zama babba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gonar masaraNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kaddamar Da Rigar Da ‘Yan Saman Jannatinta Za Su Sanya Yayin Gudanar Da Bincike A Duniyar Wata

Next Post

An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

6 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.