• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya An Noma Masara Da Tsadar Gaske A Bana – Shugaban Manoma

by Abubakar Abba and Sulaiman
10 months ago
in Noma Da Kiwo
0
tela maize
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bukaci matakan gwamnati uku na kasar nan, su mayar da hankali kan bunkasa noman rani.

 

Shugaban Kungiyar Manoman Masara, don samun riba na yankin Arewa Maso Gabas; Alhaji Adamu Muhammad Makarfi ne ya yi wannan kira.

  • Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan
  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a Kaduna, Makarfi ya yi nuni da cewa; ya zama wajibi a samar da kyakkyawan tsari, idan kuma ba haka ba; ba mu san irin abin da zai faru a wannan kasa nan gaba ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

Da yake yin tsokaci kan tsarin da gwamnatin tarayya ta fito da shi na dakile ‘yan kasuwar kasar waje zuwa gonakin manoma, don saye amfanin gonar da suka noma kai tsaye; ya ce; wannan tsari abin a yaba ne.

 

Sai dai, Makarfin ya sanar da cewa; gwamnatin ta makara wajen daukar wannan mataki, domin tuntuni ya kamata a ce an yi wannan tsari.

 

Har ila yau, a kan kakar noman bana kuwa; Makarfin ya bayyana yadda suka sayi takin zamani da tsada a noman Masarar bana da suka yi.

 

A cewar tasa, tsadar takin yasa; musamman kanannan manoman Masara Jihar Kaduna, ba su samu damar iya sayen takin ba; ballantana su noma ta.

 

Ya ce, a bana farashinsa ya ninka; hatta magungunan feshi na kwari ko na kashe Ciyawa da kudin kwadago, dukkaninsu kudaden sun karu.

 

Ya ci gaba da cewa, haka nan ambaliyar ruwan sama da aka samu a wasu jihohin, kamar Borno, Jigawa da sauransu; hakan ya sake jawo wa wasu manoman yin asara.

 

Ya kara da cewa, “A matsayina na manomi, bukatarmu ba a sayar da amfanin gona da tsada ba, amma duk da haka; ba za mu so a ce manoma sun yi asara ba, domin asarar manoma; asara ce ga kasa baki-daya”, in ji shi.

 

Kazalika, ya yi nuni da cewa; duk inda aka ce manomi ya yi noma ya samu faduwa, babban abin da ake jin tsaro; musamman manyan manoma da yawancinsu ke yin noma, don riba; idan suka fadi to fa akwai matsala, domin akasarinsu na ciwo bashi ne a bankuuna; domin yin noman da kuma kudin ruwan da ake dora musu, asarar za ta yi musu yawa.

 

Shugaban ya ci gaba da cewa, idan manyan manoma ba su yi noma a kasar nan ba, za a samu karancin abinci; hakan ne yasa za ka ga ana yin kira a je a sayo abinci daga kasashen ketare, wanda kuma idan aka yi hakan; ko shakka babu Nijeriya za ta iya yin asara mai yawa, wanda ka iya durkusar da tattalin arzikinta.

 

A karshe, ya bayyana cewa; idan har za a sayo Masara a kasar waje ba tare da an noma a cikin gida ba, akalla za a iya yin asarar kimanin Naira tirilyan goma; inda ya yi nuni da cewa, idan ba a bai wa manoman kasar nan taimakon da ya dace ba; karamar matsala ce za ta iya zama babba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gonar masaraNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kaddamar Da Rigar Da ‘Yan Saman Jannatinta Za Su Sanya Yayin Gudanar Da Bincike A Duniyar Wata

Next Post

An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

Related

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

6 days ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

6 days ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

3 weeks ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

3 weeks ago
Next Post
An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.