ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya An Noma Masara Da Tsadar Gaske A Bana – Shugaban Manoma

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
tela maize

An bukaci matakan gwamnati uku na kasar nan, su mayar da hankali kan bunkasa noman rani.

 

Shugaban Kungiyar Manoman Masara, don samun riba na yankin Arewa Maso Gabas; Alhaji Adamu Muhammad Makarfi ne ya yi wannan kira.

ADVERTISEMENT
  • Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan
  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a Kaduna, Makarfi ya yi nuni da cewa; ya zama wajibi a samar da kyakkyawan tsari, idan kuma ba haka ba; ba mu san irin abin da zai faru a wannan kasa nan gaba ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Da yake yin tsokaci kan tsarin da gwamnatin tarayya ta fito da shi na dakile ‘yan kasuwar kasar waje zuwa gonakin manoma, don saye amfanin gonar da suka noma kai tsaye; ya ce; wannan tsari abin a yaba ne.

 

Sai dai, Makarfin ya sanar da cewa; gwamnatin ta makara wajen daukar wannan mataki, domin tuntuni ya kamata a ce an yi wannan tsari.

 

Har ila yau, a kan kakar noman bana kuwa; Makarfin ya bayyana yadda suka sayi takin zamani da tsada a noman Masarar bana da suka yi.

 

A cewar tasa, tsadar takin yasa; musamman kanannan manoman Masara Jihar Kaduna, ba su samu damar iya sayen takin ba; ballantana su noma ta.

 

Ya ce, a bana farashinsa ya ninka; hatta magungunan feshi na kwari ko na kashe Ciyawa da kudin kwadago, dukkaninsu kudaden sun karu.

 

Ya ci gaba da cewa, haka nan ambaliyar ruwan sama da aka samu a wasu jihohin, kamar Borno, Jigawa da sauransu; hakan ya sake jawo wa wasu manoman yin asara.

 

Ya kara da cewa, “A matsayina na manomi, bukatarmu ba a sayar da amfanin gona da tsada ba, amma duk da haka; ba za mu so a ce manoma sun yi asara ba, domin asarar manoma; asara ce ga kasa baki-daya”, in ji shi.

 

Kazalika, ya yi nuni da cewa; duk inda aka ce manomi ya yi noma ya samu faduwa, babban abin da ake jin tsaro; musamman manyan manoma da yawancinsu ke yin noma, don riba; idan suka fadi to fa akwai matsala, domin akasarinsu na ciwo bashi ne a bankuuna; domin yin noman da kuma kudin ruwan da ake dora musu, asarar za ta yi musu yawa.

 

Shugaban ya ci gaba da cewa, idan manyan manoma ba su yi noma a kasar nan ba, za a samu karancin abinci; hakan ne yasa za ka ga ana yin kira a je a sayo abinci daga kasashen ketare, wanda kuma idan aka yi hakan; ko shakka babu Nijeriya za ta iya yin asara mai yawa, wanda ka iya durkusar da tattalin arzikinta.

 

A karshe, ya bayyana cewa; idan har za a sayo Masara a kasar waje ba tare da an noma a cikin gida ba, akalla za a iya yin asarar kimanin Naira tirilyan goma; inda ya yi nuni da cewa, idan ba a bai wa manoman kasar nan taimakon da ya dace ba; karamar matsala ce za ta iya zama babba.

Masara
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
Masara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.