ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya An Noma Masara Da Tsadar Gaske A Bana – Shugaban Manoma

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
tela maize

An bukaci matakan gwamnati uku na kasar nan, su mayar da hankali kan bunkasa noman rani.

 

Shugaban Kungiyar Manoman Masara, don samun riba na yankin Arewa Maso Gabas; Alhaji Adamu Muhammad Makarfi ne ya yi wannan kira.

ADVERTISEMENT
  • Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan
  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a Kaduna, Makarfi ya yi nuni da cewa; ya zama wajibi a samar da kyakkyawan tsari, idan kuma ba haka ba; ba mu san irin abin da zai faru a wannan kasa nan gaba ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Da yake yin tsokaci kan tsarin da gwamnatin tarayya ta fito da shi na dakile ‘yan kasuwar kasar waje zuwa gonakin manoma, don saye amfanin gonar da suka noma kai tsaye; ya ce; wannan tsari abin a yaba ne.

 

Sai dai, Makarfin ya sanar da cewa; gwamnatin ta makara wajen daukar wannan mataki, domin tuntuni ya kamata a ce an yi wannan tsari.

 

Har ila yau, a kan kakar noman bana kuwa; Makarfin ya bayyana yadda suka sayi takin zamani da tsada a noman Masarar bana da suka yi.

 

A cewar tasa, tsadar takin yasa; musamman kanannan manoman Masara Jihar Kaduna, ba su samu damar iya sayen takin ba; ballantana su noma ta.

 

Ya ce, a bana farashinsa ya ninka; hatta magungunan feshi na kwari ko na kashe Ciyawa da kudin kwadago, dukkaninsu kudaden sun karu.

 

Ya ci gaba da cewa, haka nan ambaliyar ruwan sama da aka samu a wasu jihohin, kamar Borno, Jigawa da sauransu; hakan ya sake jawo wa wasu manoman yin asara.

 

Ya kara da cewa, “A matsayina na manomi, bukatarmu ba a sayar da amfanin gona da tsada ba, amma duk da haka; ba za mu so a ce manoma sun yi asara ba, domin asarar manoma; asara ce ga kasa baki-daya”, in ji shi.

 

Kazalika, ya yi nuni da cewa; duk inda aka ce manomi ya yi noma ya samu faduwa, babban abin da ake jin tsaro; musamman manyan manoma da yawancinsu ke yin noma, don riba; idan suka fadi to fa akwai matsala, domin akasarinsu na ciwo bashi ne a bankuuna; domin yin noman da kuma kudin ruwan da ake dora musu, asarar za ta yi musu yawa.

 

Shugaban ya ci gaba da cewa, idan manyan manoma ba su yi noma a kasar nan ba, za a samu karancin abinci; hakan ne yasa za ka ga ana yin kira a je a sayo abinci daga kasashen ketare, wanda kuma idan aka yi hakan; ko shakka babu Nijeriya za ta iya yin asara mai yawa, wanda ka iya durkusar da tattalin arzikinta.

 

A karshe, ya bayyana cewa; idan har za a sayo Masara a kasar waje ba tare da an noma a cikin gida ba, akalla za a iya yin asarar kimanin Naira tirilyan goma; inda ya yi nuni da cewa, idan ba a bai wa manoman kasar nan taimakon da ya dace ba; karamar matsala ce za ta iya zama babba.

Masara
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Masara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

An Bude Bikin Al’adun Confucius Na Kasa Da Kasa Na Sin Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.